Showing posts with label Hausa Novel. Show all posts
Showing posts with label Hausa Novel. Show all posts

Thursday 29 November 2018

Hausa Novel: K'ARSHEN WAHALA ( By Aishat A Muh'd)

November 29, 2018 0

🍀🍀☘☘🍀🍀
   *K'ARSHEN WAHALA*🍀🍀☘☘🍀🍀




            *NA*

     *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘

*GODIYA*
_Godiya ga Allah {SWA} da ya bani ikon fara rubuta wannan littafin nawa tsira da amincin Allah su k'ara tabbata ga Annabi Muhammad {SAW}_.....


  *JAN HANKALI*
 _Wannan littafin banyi shi don wani ba ko wata nayi shine don fad'akarwa,nishad'antar wa don hka a d'auki abu mai amfani a bar mara amfani abin da yake kuskure Allah ya yafe min,Allah yabamu ikon aikata dai dai a rayuwar mu ameeen_......

*ZUWA GA MASOYA NA*
_godiya mai yawa a gare ku masoya na,nima ina kaunar ku_.


*BAZAN MANTA DA KE  BA*
_my cwt Sadeey  S Adam {saNaz Deeyah} da irin k'warin gwiwar da kike bani da soyayyar da kike nuna min don *Adalilin son* da kike nuna min na kai hka Allah ya bar mu tare_.......


*~pg 1~*


   Yanayin unguwar irin unguwar masu hannu da shuni ce gwamna road a garin kd,family d'in gdn gaba d'aya suna xaune a k'ayataccen falon su hira sosae suke da kagan su kasan happy family ne  ....

   Alhaji sa'eed haruna kenan da matar shi hajia maimuna sai yaran su safah itace babba sai nauwarah da k'aramin su saleem,su kadai Allah ya basu don sun ma fitar da ran sake haihuwa tun da saleem ya kai 7yr's da haihuwa, suna matuk'ar kaunar 'ya'yan su sosae ana cikin hira caraf nauwarah tayi magana cikin shagwaba take cewa

    " _Abba gaskia ina son idan na kammala secondary schl malaysia nake son ka sama min university_"

Dariya abban yayi irin ta manya sannan yace
    " _nauwarah 'yar gidan Abba kada Ki damu Insha Allah xan cika miki wannan burin ke dai Allah yasa muna raye ki kwantar da hankali ki_"

Cikin tsananin murna tace
  " _Ameeen my abba na_"

Har ta bud'e baki  xata sake magana safah ta watsa mata harara kamar idon ta ya fad'o tace

  " _tabbb Lallai yarinyar ae yanda nayi karatu a 9ja ke ma hka xakayi ba inda xaki je_"

 Turo baki tayi cike da shagwaba tace " _uhm kaji aunty safah da wani xance kuma bayan ynx agaban Ki abba ya amince min koh abb?_"

  " _k'warai da gaske nauwarah ta haske mai kyau hasken idaniya ta da ixinin Allah xaki je ke dai ki dage da karatu kmr yanda na san ki_"

Wani tsalle ta buga tana ihun murna yayin da safah ta xumburi baki cike da haushi tace

  " _dallah malama kin dame mu da ihu idan baki shiru ba ynx na tashi na bubbuge bakin ki_"

Murgud'a mata d'an k'aramin bakin ta tayi cike da tsiwa tace

  " _kaji mu da aunty safah nan ina ruwan ki da ihu ba Naga dai murna nake_"

Axuciye safah ta tashi tayo kanta aikuwa da gudu ta b'uya a bayan ammin ta tana mata gwalo abba da saleem da ammi dariya kawai suke yi musu hannu tasa xata fisgo ta da sauri ammi ta tare tana cewa

 " _a'a safah yi hak'uri ki kyale ta kinsan yarinya ce kuma naga ae murna take_"

 " _amma dai ammi Kina kallo gwalo take yi min_"

Da sauri ammi ta juya bayan ta ae kuwa taga nauwarah gwalo take mata cikin fad'a ammi tace

  " _bana son hka nauwarah baki ga yayar Ki bace ji nake d'axu kika gama bibbige min saleem don ya tab'a miki phone d'in ki_"

" _tohh ammi na dai na yi mata_"
Ta fad'a kamar xata fashe da kuka murmishin mugun ta safah ta saki tare da cewa

  " _yarinya xaki xo ki same ni ne_"
Idon ammi ta faka ta Murgud'a mata baki yanda take Murgud'a bakin da ka gani kasan ta riga ta saba da hkan....


Ko _10 mints_ ba'a yi ba na hango nauwarah kusa da safah tana wani marairaice fuska tare da langab'e kai alamar tana son wani abu safah tana kallon ta ta gefen ido kamar xata tuntsire da dariya hka take ji dakyar ta iya  danne dariyar bata kula ta ba ta Kalli inda saleem yake tace

" _saleem dauko min maltina a frige mai sauk'in sanyi_"

Ae Kafin ta rufe bakin ta da gudu nauwarah ta nufi frige ta d'auko mata maltina ta Mik'o mata hararar ta safah tayi tare da cewa

  " _na ambaci sunan ki ne ae Naga saleem na aika_"
Murgud'a mata baki tayi cikin k'uluwa safah tace " _au  Murgud'a min baki kike_"

Da sauri nauwarah ta dafe bakin ta cikin marairaicewa tace
 " _hba aunty safah na mance ne I'm so sorry baxan k'ara ba ki karb'a kisha Kinsan baxan ji dad'i ba Idan baki karb'a ba plsss_"

Gaba d'aya falon aka kyalkyale da dariya ita kuma sai wani lalangab'e kai take da yake safah tana masifar son kanwar ta bata son abin da xai b'ata mata rai yasa ta karb'a ae kuwa ta rungume ta tana dariya ba wanda bai yi dariya ba a wajen.....

Tana shan maltina nauwarah cikin K'aramar murya tace " _Aunty safah yaushe xaki kaimu shopping ne gaskia kayan kwalliya na sun kusa k'are wa_"
Harara ta xabga mata kafin tace

 " _baxa ajeba sai ki nemi driver ya kai ki_"

" _Kaiiii aunty baxa ki kai ni ba don Allah ki taimaka plsss_"

Abba ne yace " _aunty safah ayi hak'uri akai ta mana_"

Hannu tasa ta dungure mata gaba d'aya aka tuntsire da dariya kafin tace " _kinci darajar abba yarinya_"

Cike da d'oki da murna tace" _xaki kai ni my cwt sister?_"

  " _xan kai Ki Insha Allah gobe 'yar cwt k'anwata_"

Murmishi tayi har dimple d'in ta ya lotsa tayi kissing d'in ta a kumatu tare da fad'in
  " _thank you so much my aunty safah_"

Saleem yace " _har dani xa'a je koh aunty safah?_"
Harara nauwarah ta xabga mishi tare da cewa " _baxa'a da kai ba yaro_"

B'ata rai yayi tare da cunkushe fuska kamar xai fashe da kuka da sauri ammi tace " _kada ma kayi kuka dole aje da kai_"

Xumbura baki nauwarah tayi tare da tashi ta nufi bedroom.......




    *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘
[2/19, 4:54 PM] Aishat A muh'd ✍🏻: 🍀🍀☘☘🍀🍀
  *K'ARSHEN WAHALA*🍀🍀☘☘🍀🍀




            *NA*

    *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘





*~pg 2~*



  *WANE NE ALHAJI SA'EED HARUNA???*


 'Dan asalin garin kaduna ne a wata unguwa tudun wada anan mahaifan sa suke mahaifin sa Baffah haruna yana da rufin asirin shi dai dai gwargwado da matan sa 2 inna zainab ita ce babba tana da yara 2 sa'eed da mace safiyya sai inna larai d'an ta d'aya sunan shi salisu da yake Allah bai bashi yawan xuri'a ba......


  Baffah haruna yana matuk'ar kokari wajen kyautata wa iyalan shi da bawa yaran shi tarbiyya ta k'warai sai dai kwata kwata ba'a xaman Lfy a tsakanin matan na shi babu jituwa Ko Kad'an....

  Inna zainab mace ce mai hak'uri da kau da kai akan komai yayin da inna larai bata da hak'uri ko Kad'an saboda tana ganin baffah haruna ya fisan su zainab da yaran ta alhalin yana iyakar kok'ari wajen kwatan ta adalci a tsakanin matan shi da 'ya'yan sa.

   Axahirin gaskia yafi k'aunar zainab da yaran ta saboda sun fi mishi biyayya musamman sa'eed yana matuk'ar kaunar shi yaro ne mai hankali da nutsuwa bai dauki duniya da xafi ba shi yasa uban yake son shi sa6anin salisu da ya dauko halayar mahaifiyar shi akwai shi da mugun hassada da kyashin wani yayi abu shi bai yi ba baffah haruna yayi fad'an yayi nasihar duk a banxa don hka kawai ya kyale shi yana mishi addu'ar Allah ya shirya shi....



         *******
  Bayan sa'eed ya kammala schl ya samu aiki a wani company albarkar iyaye da addu'ar su tare da yanda yake taimakon mutane yake gani saboda ganin yanda Allah yake bud'a mishi harkokin sa yana samu sosae ganin hka yasa kishi da hassada a xuciyar salisu saboda ganin sa'eed ya fishi samu ba shi kadai ba har inna larai.

   Shi kuwa bawan Allah sa'eed ba ruwan shi sau tari sai ya dauki kudi ko yayi musu d'inki tare ya bashi don yana kaunar d'an uwan shi duk da hka salisu bai fasa nuna mishi bakin cikin yafi shi samu don salisu kullum a tunanin shi yafi d'an uwan shi samu amma Allah bai bashi nasarar hkan ba.

  Safiyya kuwa dakyar baffah haruna ya barta ta gama secondary schl ya aurar da ita d'an kasuwa lokaci d'aya Allah ya had'a soyayyar su don hka da akayi bincike aka ga yana da Kyan hali ba ada'u lkc ba akayi auren aka kaita unguwar malali lfy suke xaune da mijin ta....

  Ahka lokaci yake tafiya har sa'eed ya had'u da maimuna irin kyakkyawan  nan ce don gaskia akwai ta da kyau ba k'arya 'yar ogan shi ce Allah ya had'a soyayyar su da yake ogan nashi yana son sa'eed sosae jinin su ya had'u don hka ba'a samu matsala a ko'ina ba akayi auren...

  Amarya maimuna ta tare a gidan sa'eed suna rayuwar su cikin kwanciyar hnkl hkan yasa salisu bakin ciki sosae ta yanda akayi ya auri wannan kyakkyawar kamar balarabiya tun ganin shi na farko yaji yana masifar son ta kamar me anan ya kuduri wani mugun nufi a xuciyar shi..........



    *BAYAN WASU SHEKARU*............

  Abubuwa da yawa sun faru a wad'annan Shekaru Alhaji sa'eed ya samu karuwar haihuwa mata 2,safah ce ta farko sai nauwarah da batafi 3yrs ba sai tsohon cikin da take dashi haihuwa yau ko gobe...

  Ana cikin hka salisu yaxo gdn yayan shi cike da bacin rai yana shiga falon ya had'a ido da maimuna tana xaune a falon tasha kwalliya kai  ba kace ta haifi safah da nauwarah ba ae tuni yaji duk bacin ran da ya shigo dashi ya yaye washe hak'ora ya shiga yi cikin dariya yace

 " _uwar gida ran gida maman safah da nauwarah kina Lfy???_"

  Shiru tayi kamar baxa ta amsa ba saboda kwata kwata jinin su bai had'u da salisu ba ta tsane shi saboda yanda yake yiwa Baffah haruna da mijin ta sa'eed rashin kunya a dak'ile ta amsa da

  " _lfy qlau nake_"

 Bai damu da yanda take b'ata fuska ba ya samu wuri ya xauna cikin murmishi kamar mai tallan maclean yace

  " _dftn wannan siririn mijin naki ya nan Don wurin shi naxo_?

A fusace tace  " _Wannan wanne irin rashin mutunci ne salisu kaxo har gida na a gaba na kana ciwa mijina mutunci tohh wlh baxan yarda ba idan ka k'ara xan dau mataki akan ka_?

  Ranshi idan yayi dubu ya b'aci amma da yake d'an duniya ne ya k'ak'alo murmishin dole yace " _okay ayi min afuwa baxan k'ara ba matar babban yaya d'an yi min magana dashi don Allah_"

  Sai da ta saki tsaki kafin ta mik'e ta nufi stairs shi kuma ya bita da kallon yana had'yar yawu tare da lashe leb'en shi yana tunanin abubuwa da yawa a ran shi....

  Bata da deba yaji tahowar su don yana jin dariyar su k'asa k'asa alamar magana mai dad'i suke fad'a wa junan su wani abu yaji ya tokare shi a mak'wogaron shi ya fad'a tunani sai da yayan shi ya dafa mishi Kafad'a sannan ya dawo hayyacin shi ya saki wani huci mai zafi kafin ya fara magana ba alamar ma xai gaida yayan nashi yace

" _daman yarinyar da xan aura ce na samu sai old man yace bai yarda ba to nasan yafi jin maganar ka shine nake son kayi mishi magana don gaskia baxan iya hak'uri da ita ba idan yak'i yarda xan gudu a neme ni a rasa sunan yarinyar binta lawan shana_"

 Yana gama maganar ya kad'e rigar shi ya fice daga falon ya bar sa'eed kamar an dasashi a wajen cike da tunanin abin da salisu yake kok'arin janyo musu..........






   *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘
[2/19, 4:54 PM] Aishat A muh'd ✍🏻: 🍀🍀☘☘🍀🍀
  *K'ARSHEN WAHALA*🍀🍀☘☘🍀🍀




             *NA*

    *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘





*~pg 3~*



Dafa mishi kafad'ar akayi da sauri ya juyo sai yayi arba da kyakkyawar fuskar matar shi tana yi mishi Murmishi amma ganin tarin damuwa a fuskar gwarxon mijin ta nan da nan fuskar ta ta rine xuwa tarin damuwa cikin muryar kwantar da hankali tace

  " _ya kai mijina menene dalilin shigar ka damuwa?_"

Kamo hannun ta yayi ya xaunar da ita kan kujera shima ya xauna yana fuskantar ta sai da ya sauke numfashi Kafin yace

   " _ba wanine ya sani shiga damuwa ba illa salisu da yake kok'arin janyo wa kanshi abin da yafi k'arfin shi?_"

 " _me yake kok'arin janyo_?"

" _wai aure yake son yi baffah bai amince da yarinyar ba shine yaxo wae baffah yafi jin magana ta nayi mishi mgn idan ba hka ba xa'a neme shi a rasa_"

Shiru tayi na d'an lokacin k'alilan tukunna ta sauke ajiyar xuciya tace

    " _idan yak'i yarda ya hak'ura da yarinyar toh ku kyale shi ya aure ta sai mu taya shi da addu'a kada ya gudu kasan xai aikata hakan_"

Shiru yayi na 'yan Mintuna Kafin yace
  " _xamu yi mgn da baffah ngde da shawarar da kika bani idan Allah ya K'addara wannan auren Shikenan fatan mu Allah ya xa6a mishi abin da yafi alkhairi amma salisu sai a hankali ya fiye rigima wlh Kinsan wacce yarinya ce kuwa?_"

Girgixa kai tayi alamar a'a " _toh 'yar gdn lawan Shana ce_"

 Zaro ido tayi Kafin ta gid'a kai tace " _Allah ya kyauta amma sam bai yi dace da mace ta gari ba_"

" _Ameeen dai amma shi ae idon shi ya rufe bae ga hkan ba_"



*WANE LAWAN SHANA*

    Alhaji lawan Shana shine cikakken sunan shi don anfi sanin shi da lawan Shana sunan shana ya samo asali daga lokacin samartakar shi saboda tantirin d'an duniya ne mai son ya shana a duniya yana d'an rufin asiri ba laifi akwai masifar son yaga ya tara dukiya matan shi 4 da tarin yara har 13 gaba d'aya tarbiyyar su sae a hankali....

  Acikin su akwai wata binta Tana da kyau ba laifi sai dai maimuna tafi ta kyau nesa ba kusa ba gaba d'aya ta kwashe halin baban ta _100  percent_ shi yasa yake masifar son ta a 'ya'yan shi komai xata iya aikata wa don ta samu kud'i a kaduna polytechnic take karatu duk da bata bashi mahimmanci irin 'yan d'umama benci ne,ita ta fara cewa tana son salisu don da alama xata huta a gdn shi baya aurar da yaran shi talaka sai mai kud'i idan talaka ne mai yaci balle ya bawa 'yar shi kaji shi sai kace shi ba talakan bane ya mance Allah ne mai axurta bawan shi......


An kai ruwa rana kafin baffah ya amince don salisu akwai shi da kafe ya da hka akayi auren duk 'yan uwan shi basa so daga shi sai babar shi inna larai...

Bayan 2weeks da bikin salisu maimuna ta haihu yaro yaci suna saleem........



           *******

   *MUN DAWO LABARI*

  A kayattaccen bedroom d'in su na hango nauwarah ta k'ure volume d'in tv tana jin wak'ar da deepika tayi a film d'in rasleela ram Leela kamar wadda tayi practice d'in rawar hka take yi ta iya rawar sosae kamar itace deepika d'in {lol}

 Gaba d'aya ta cikawa safah kunne da kunne da k'ara gashi karatu take saboda gobe tana da test a schl gaba d'aya tabi ta dame ta a fusace tace

  " _wannan kuma sabon wani wulak'ancin ne nauwarah ina karatu kin samu kin k'ure volume_"

Sae da ta Murgud'a mata baki Kafin tace  " _hba aunty safah don Allah ki kyale ni nayi nishad'i man Kinsan ina bala'in son wak'ar nan_"

" _ki tafi falo mana kiji_"

Zaro ido tayi tana cewa " _tabbb kina so ammi ta doke ni tana falo fah a xaune_"

Tsaki safah ta ja kafin ta tashi afusace tayi kan nauwarah da gudu tayi hanyar fita daga d'akin sai taga ashe kid'an ta kashe ta juyo Tana kallon nauwarah tayi wuk'i wuk'i da ido hararar ta tayi kafin ta juya ta xauna tana cewa

 " _sai tsabar tsokana amma tsoro fal ciki_"

Ta dauki buk d'in ta tana dubawa ganin hka yasa nauwarah ta lalla6a tana Xumbura baki taje ta jona socket d'in da safah ta kashe iya k'uluwa safah ta k'ulu ta tashi da sauri tayi kan nauwarah ae kuwa ta kwasa da gudu sai falo ita ma safah ta bita da gudu sai ganin su ammi tayi kamar wad'anda aka cillo da sauri ta mik'e Tana cewa

" _lfy safah me yafaru?_"
nauwarah tana ihun _Wayyo Mumy Ki taimaka min aunty safah xata Duke ne_"

Duk tabi ta cikawa ammi kunne da ihu gashi ta ruk'unk'u ne ta cikin fusata tace
" _ammi wannan mara kunyar yarinyar  ce ina karatu ta ishe ni da jin wak'a duk ta hanani karatu_"

Ammi tace " _baki da kunya nauwarah koh safah kike yiwa hka ba yayar ki ce ba  ki bata hak'uri kuma kada Ki sake na gaya miki_?

Cikin murya kamar xata fashe da kuka tace " _I'm so sorry my aunty safah na dai na amma kada Ki doke ni plss_"

K'wafa tayi sannan ta bar wajen nauwarah ta fito daga bayan ammi tana sakin ajiyar xuciya can kuma ta kyalkyale da dariya tace " _ohhh thank god to save me_"
Harara ammi ta watsa mata sum sum ta shige tana dariya.............






     *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘
[2/19, 4:54 PM] Aishat A muh'd ✍🏻: 🍀🍀☘☘🍀🍀
 *K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀




           *NA*

   *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘




*~pg 4~*


   Xaune suke a falo Alhaji salisu da Alhaji lawan sai hajia binta suna yin wasu maganganu da alama maganar da suke yi ta sirri ce ba kowa ake so yaji ba can naji muryar Alhaji salisu yana cewa
  " _ya kamata mu gama samu mafita don ni wlh na gaji da ganin shi awannan duniyar ta mu da shi da wad'annan 'yan iskar 'ya'yan nashi don ni wlh kishi nake dasu kamar yanda nake kishi da uban su_"

  Hajia binta ta xabga mishi wata harara kamar idon ta ya fad'i k'asa taja wani shegen tsaki a fusace tace

  " _wlh salisu baka da mutunci kana tunanin idan ina raye xaka auri wannan shegiyar matar mai kama da aljanu, toh wlh tun wuri kama cire son ta daga xuciyar ka idan ba hka ba sai na.................. "

 Kafin ta K'arasa fad'in hka Alhaji lawan ya daka mata wata tsawa ba shiri ta hadiye sauran maganar ta ta fuska a d'aure yace

  " _na fuskanci baku damu da abin da ya tara mu anan ba toh wlh xan tashi na tafi tunda baku tanadi abin fad'a ba,ke kuma binta idan ba rashin hankali da tunani ba ina ruwan ki da son ta da yake yi ke dai ba kud'i kike so xaki wani cikawa mutane kunne da ihu_"


Cike da rashin kunya tace " _ae bani kad'ai ce mai son kud'in ba naga Har kafi ni son su taya xae dunga maganar wannan mai kama da aljanun_"


  " _yayi d'in don uban ki tunda ke baki da mutunci ni uban Ki kike gaya wa hka ko_"

 Alhaji lawan yayi maganar a fusace har ta bud'e baki xatayi magana Alhaji salisu ya dakatar da ita da hannu Kafin ya d'ora da cewa

  " _don ynx wannan bata ta so ba ni kawai so nake a fara kawar dashi tukunna_"

Nan kowa ya fara kawo tashi shawarar idan suka duba sai aga batayi ba sun d'auki wajen _1 hour_ suna magana da K'arshe har xasu tashi da xummar kowa yaje yayi tunani akai sai har sun mik'e tsaye sai suka ga Alhaji lawan ya kwashe da dariyar mugunta ya dad'e yana dariya kafin ya tsaya su kuma suka xuba masa ido suna kallon shi cike da mamakin abin da yasa shi dariya dakyar ya tsagaita da dariyar Kafin yace

  " _kun ga ina dariya kamar na haukace ko toh mafitah na samo mana kuma mai sauk'in gaske ku kawo kunnen ku kuji saboda ina tsoron kada iska ta kwashi sauti  na aji koh yah_"

Ae kuwa da sauri suka mik'a mishi kunnen su ya d'au tsahon _10 mint_ yana magana Kafin lokaci d'aya su kwashe da wata mahaukaciyar dariya ke bakace d'an adam ne ke yi ba daga hka duk suka tarwatse xuciyoyin cike da farin ciki........



         *********

   Sanye take cikin wata gown d'in shadda dark blue tasha make up Sosae tayi masifar yin kyau d'aurin d'an kwalin ya xauna a kanta sosae sai tayi amfani da sark'a white mai touch d'in blue a jiki ta sanya white shoes nauwarah kenan sarkin son gayu kenan suna masifar kama da ammin ta don ita ta kwashe kusan kyan nata don tafi safah da saleem kyau shi yasa abban su yafi k'aunar ta cikin takun ta kamar mai tausayin k'asa ta fito xuwa falo sai kace wata babbar mace don bata fi 16yrs ba a duniya amma idan tayi wani abun ka d'auka wata babbar ce.....

Kuma sunyi dace da iyaye don dai dai gwargwado sun basu tarbiyya suna da iIlimi na addini da na nasara mai jan kunnu wa Duk kud'in mahaifin su bai hana su tsaya wa k'in neman ilimi ba..

Tana k'araso wa falo ta tarar da ammi sai saleem suna xaune suna kallo cike da shagwaba ta kwanta a jikin ammi tace

 " _ammi Har ynx aunty safah Bata dawo daga schl ba_"

 " _ehhh Kinsan lectures d'in yamma ne da ita yau_"

Ammi ta bata amsa turo baki tayi gaba sannan tace  " _tabbb ammi anya xan iya kai wannan time d'in a schl kuwa ae gudu wa xanyi_"

Harar ta ammi tayi kafin tace " _daman ke ina xaki iya raguwa dake xan kuwa gaya wa abban ki kada ya b'ata kud'in shi a banxa ya kai Ki har malaysia karatu gwara ya barki anan_"

Marairaice fuska tayi tare da langab'e kai tace  " _ya hak'uri ammi na da wasa nake wlh kinsan yanda nake da burin yin karatu sosae kada ki fad'a wa abba plss_"

Dariya kawai tayi tana cewa " _ohh nauwarah ran da bamu a duniyar har tausaya miki nake wanda xai iya da shagwabar ki_"

Kicin kicin da fuska tayi can kuma sai ga hawaye yana xuba a fuskar ta cikin kuka tace  " _don Allah ammi ki dai na wannan xance ae rasa ku arayuwa ta nasan ba k'aramin *K'ARSHEN WAHALA* xan shiga ba_"

Sosae ta fashe wa ammi da kuka nan ta fara rarrashin ta tana cewa " _ae mutuwa tana kan kuwa nauwarah ba mai guje mata fatan Allah ya sa mu cika da imani_"

Dak'yar ta lalla6a tayi shiru har safah ta dawo daga schl suka cigaba da hira kiran sallahr mangariba ne ya tashe su daga hirar....


*12 pm*

 Innalillahi wa'inna ilaihir rajun ta farka a firgice daga wani mummunan mafarki da tayi gaba d'aya ta jik'e da gumi ta kai idon ta kan safah da take baccin ta hankali kwance shiru tayi tana tunanin abin da ta gani a mafarkin wai abban ta ne ya rasu gashi ana xaman makoki suna ta kuka ita dasu ammi daga nan ta fara......

Xumbur ta mik'e ta tsaye ganin an kunna hasken d'akin ido hud'u sukayi da abban ta sosae tayi mamakin ganin shi a irin wannan lokacin tashi tayi ta nufi wajen shi kawai ta tsaya kallon shi ta kasa cewa komae hannun ta ya kama ya  xaunar da ita a gefen bed sannan shima ya xauna a hankali yake magana don kada ya tashi safah a bacci yace

  " _kema Kinyi irin mafarkin da nayi ko na dad'e ina irin wannan mafarkin amma na yau yasha banban da na ko yaushe_"

Ita dai nauwarah kallon shi kawai take shima bai damu da irin kallon da take mishi ba ya cigaba da cewa

  " _ban tab'a gaya muku bane ko ammin ku bana gaya mata saboda ban son tashin hankali ku mak'iya sun yi min yawa nauwarah an dad'e ana bibiya ta don aga baya na na amma Allah bai basu ikon hkan don hka ina son ki kula da 'yan uwan ki da ammin ku, bana son ki fad'a wa kowa munyi magana dake wannan ya xama sirri a tsakanin mu_"

Nauwarah wadda ta kusan suman xaune bakin ta na rawa tace  " _Abba su wane? Kuma me suke so a wajen ka? Sannan ka fad'a wa police mana? Kuma ta yaya xan iya kula da ammi safah da saleem???_

Murmishi ya saki kafin yace "_xaki iya kula da su man sannan rayuwata da dukiya ta suke nema, hmm nauwarah ke yarinya ce shi yasa amman ae idan baka iya kama 6arawo ba shi ya kama ka sanar da police ma bata taso ba gobe xan yi tafiya xuwa kano wajen wani aminina akwai  maganar da xamu yi dashi na yarda da dashi fiye da yanda kike xato nasan baki san shi ba"

Abba ya d'an sauke numfashi Kafin ya cigaba da cewa  " _xan baki wata jaka tana d'auke da dukkan wata muhimmiyar dukiya ta don ku samu damar kula da kanku Insha Allah baxa su ci galaba a kanki ba kuma ina son idan Allah ya nufa sun samu galaba a kaina ku gudu xuwa kano xan rubuta miki address d'in shi gobe na baki nasan shi kad'ai xai iya taimaka muku tsakani da Allah_"

Hannun nauwarah ya kama ya damk'a mata wata jaka sannan ya rungume ta har sai da k'walla ta xubo mishi tashi yayi tsaye tare da cewa

" _Allah yayi muku albarka ya k'are min ku a dukk inda kuke_"

Bud'e baki nauwarah tayi xata yi mgn da sauri yasa hannu ya rufe mata baki ya nuna mata safah dake motsi  da sauri ya fice daga bedroom d'in bayan ya kashe hasken d'akin........






   *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘
[2/19, 4:54 PM] Aishat A muh'd ✍🏻: 🍀🍀☘☘🍀🍀
 *K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀




             *NA*

  *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘




*~pg 5~*


  Tun da abban ta ya bar d'akin take xaune cike da tsoro da tashin hankali akan abin da ya sanar da ita me yasa abban ta ya yanke hukuncin sanar da ita bai sanar da ammi da safah ba ae ita tayi k'ank'anta da asanar da mata da wannan rikitaccen labarin mai kama da film Ko mafarki *ADALILIN SON* matar shi da dukiyar shi ake neman ranshi to suwaye wad'annan marasa imanin tunanin da take da kuka su suka hassada mata matsanancin ciwon kai idon ta duk sunyi jawur dasu sai rad'ad'i suke yi mata kamar an xuba barkono


Dakyar ta iya mik'e wa tsaye ta bud'e wardrobe d'in ta ajiyar jakar tayi sannan ta nufi toilet alwala ta d'aura bayan ta fito ta shimfid'a abin sallah ta fara nafilfilo batasan adadin nawa tayi ba sai da taji jiri ya fara d'aukar ta sannan ta xauna ta janyo al qur'an ta fara karatu cikin muryar ta mai d'an karan dad'i tana hka har asuba tayi tana idar da sallah bacci yayi awon gaba da ita akan abin sallahr


Wajen 10 na safe Abba ya fito cikin shirin tafiya yasha manyan kaya farare sol dasu da yake ranar juma'a ne ya xauna akan dinning table ammi tana had'a mishi breakfast ya xuba mata ido ko kiftawa ba yayi har ta gama had'a mishi ta juyo don tayi mishi magana ta ga ya xuba mata ido yana kallon ta Murmishi ta saki wanda ya dad'a fito mata da Kyan ta kafad'ar shi ta dafa sannan tace

  " _Abban safah irin wannan kallon hka Lfy?_"

Ajiyar xuciya ya saki tare da rik'o hannun ta yace " _bakomai gani nayi yau Kinyi min kyau sosae_" dariya ya bata ta kyalkyale da dariya don wannan kalmar kullum sai ya fad'a mata dariyar da take ta bashi shima dariya don hka yayi murmishi kawai kafin tace

  " _nima kayi min kyau wlh fiye da koyaushe, amman kayi sauri ka gama don nafi son ka dawo da wuri saboda bana son dare yayi muku a hanya_"

 " _an gama ranki ya dad'e_"

A hankali ya fara cin abincin yana ci yana kallon ta tun tana jin dad'in hka har ta fara jin tsoro anya wannan kallon nashi na lfy ne kafin ta samu tayi magana safah da nauwarah sun k'araso wajen suka gaida iyayen nasu cikin girmama wa gaba d'aya nauwarah jikin ta a sanyaye yake ko gayun da ake yau babu shi ta samu waje ta xauna tare da xabga tagumi ammi ta xuba mata ido kafin tace

  " _lfy qlau kike nauwarah duk Kinyi wani iri gashi Kinxo kin xabga tagumi_"

Kafin tayi magana caraf safah tace  " _wlh umma na tambaye tun d'axu tace ba komai koh tsokana ta yau bata yi ba_"

Har ta bud'e baki xatayi magana suka had'a ido da Abba yayi mata alamar kada ki fad'a musu don hka tayi murmishi yak'e tace

  " _ammi ba komai na tashi da ciwon kai ne_"

" _Allah ya sauwake kiyi maxa ki karya sai kisha paracetamol_"

Kad'an ta iya cin abinci ta ture ta xauna har abba ya gama suka mik'e tsaye don raka shi har wajen motar da xai tafi a ciki suka rakashi duk sai da ya rungume su sannan ya shiga mota driven shi har ya kunna mota sun kusa fita daga get ya bashi umarni ya dawo baya ammi suka tsaya kallon shi cike da mamakin shi sai da ya dad'a fitowa ya rungume su ya dunga kallon su gaba d'aya sun tsorata da hkan nauwarah kuwa tuni ta fara kuka ganin hka yasa ya koma mota drive yaja mota yana ta kallon su har suka fice daga gidan gaba d'aya mai gadi ya mayar da kofa ya rufe da gudu nauwarah ta shige falo tana kuka sosae ammi da safah sai saleem suka nufi falon gaba d'aya jikin su a sanyaye dakyar suka lallashi nauwarah tayi shiru safah ta vata magani bata dad'e da sha ba bacci yayi awon gaba da ita.......


Tsaye yake a K'arshen layin da alamar jiran wani abun yake ganin wata mota ta shige yasa shi sakin wani murmishin mugunta tana shigewa ya dauko wayar shi a aljihu ya kira wata number bata dad'e tana ringing ba aka d'auka cikin wata katuwar murya yace

  " _Oga an cika aiki nan d'an lokaci xakuji kyakkyawan labari_"


Daga d'aya bangaren aka kwashe da wata mahaukaciyar dariya dakyar ya tsagaita da dariyar Kafin yace
 " _aikin ka kyau mu had'u anjima da yamma a guest house d'ina mu K'arasa biyan ka_"

Daga hka ya kashe wayar cikin farinciki ya tsayar da keken napep ya shiga suka tafi..........





  *_Aishat A muh'd {Aunty}_*😘
[2/19, 4:54 PM] Aishat A muh'd ✍🏻: 🍀🍀☘☘🍀🍀
 *K'ARSHEN WAHALA*
🍀🍀☘☘🍀🍀

Friday 2 November 2018

Hausa Novel: Komai Rintsi ( By Hamagee )

November 02, 2018 0



馃尫: KOMAI RINTSI馃槍.........


Na 馃尫Hamagee馃尫馃摎


0鈨�1鈨�

    Yarinya yar kimann 4yrs ce  ta saki kuka sakamakon rankwashin da tasha gun wanta,"tashi ki tafi gun uwarki" ya fadi da karfi wanda ya qara kidimar da yarinyar ta tashi da gudu ta nufi side dinsu tana kuka.


  "Me ya sameki Fadwa??"batace komai ba illa sautin kukan da ta qara nan da nan ran momyn ta ya baci dan tasan ba wanda zae sata kuka inba yayyanta ba.Tace "yi shiru ki fada mun, kinyi rashin kunya kou? "Ta gigiza mata kai tace "ya faruk neh ya bugen" sae ta sake fashewa da wani sabon kukan.Wae yarinya qarama har ta san ana mana ba daedae ba, momyn ke fada a ranta ta janyo ta jikin ta tana rarrashin ta "kiyi shiru kinji baby nah zan rama mki"tayi ta lallaminta dae da qyar ta samu tayi shiru har tayi bacci a cinyarta.

 
     Nan momy ta tashi tayi sama da ita, ta kaita dakin ta shimfidata kan gado sannan ta nufi toilet tayi alwala tazo tayi sallahn la'asar ta soma koro adduo'i kan Allah ya raya mata ya da imani sannan Allah ya zabanmata miji na gari ko zataji dadi nan gaba dan gaskya yan uwanta basu sonta ko kadan.Bayan ta idar ta tofa sannan ta tashi ta hau gadon itama,a gefen fadwan ta dan kishingida tana shafa kanta a hankali tana tunani iri*2....


   
    A side din su Ya faruk kuma ummansu tana sauqowa daga sama ta fara fada "wace maciyaciyar yarne ke cikamun kunne da kuka ina bacci?" Tasleem tace "umma wa kuwa banda wancan shegiyar"  (wae kuji yar uwarta take kira shegiya hayan ubansu daya, Allah ya qara mana tsoronshi ya kuma sa mu dace "Ameen").Umman tace "yar iskan yarinya,mema ya kawota nan neh, inta sake zuwa ku mata dukan tsiya nina baku wannan izinin" sannan ta ja tsaki mtswww ta koma daki ta turo qofa da qarfi....n

   Wacece Fadwa da yan uwanta??? Mujee zuwa......nn
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: KOMAI RINTSI......馃槍



  By 馃尫Hamagee馃尫馃摎馃摑


0鈨�2鈨�

  Dr. Mahmud Adam sunan mahaifin su fadwa kenan, yanada mata biyu umma wacce itace uwargidansa sae momyn fadwa ce amarya.Iyayen sa wato haj.ameena da alhj.Adam kabeer...Su biyu suka haifa wato shida wansa Barr.Khaleed Adam, sun taso cikin jin dadi da kulawa da juna, iyayensu na matuqar son su da nuna musu tarbiyya, alhj.Adam nada kudi kwarae da gaske,sanaarsa saeda motoci neh, kuma yanada gidajen mai da dama kusan kowane state a Nigeria yanada gidan mai,  hakan yasa yayansa suka taso cikin gata da wadata, sunyi karatunsu na nursery da primary a nan Nigeria sae sukaje London yanda suka qare karatunsu na jamia,Dr.Mahmud ya karanci medcine wanda ya zama consultant shikuma Brr.Khaleed ya karanci law.Tsakaninsu bbu wani nisa a shekaru bae wuce biyu zuwa biyu da rabi ba tsakani kasancewar iyayen basu haihu na fari da wuri ba.wannan kenan


 
   Bayan sun dawo gida neh Barr.Khaleed wato babban dan alhj.Adam ya hadu da yarinya yace yana so me suna Rauda.Rauda yarinya me hankali da nutsuwa gami da tarbiyya ga girmama na gaba, wanda hakan yasa yaji ta kwanta masa a rae, tanada matuqar kyau dan yar niger ce zama neh ya kawo su nan Nigeria ita da iyayenta,am mai transfer neh zuwa nan Yola...


   Baa wani dau lokaci ba soyayya mai qarfi ta shiga tsakanin Khaleed da Rauda har ta kasance manya sun shigo maganar an sanya ranar bikin su.Murna wajen iyayen su baa magana, bayan sunyi aure sae suka koma FCT  wato Abuja da zama amma suna da gida a nan Yolan, gidan amarya yasaha kyau da haduwa ga girma ga kayan alatu kasancewa itama iyayenta masu hali neh daedae gwargwado...


   Bayan bikinsu da shekara guda Allah ya bata ciki ta haifo danta kyakkyawa mai kama da ita aka sa mishi sunan Abba wato Muhammad Adam.Munra wajen dangi da abokan arziqi baa magana, anyi suna mai raeda lfya an watse...

    Dr.Mahmud neh kwance a dakinsa yana waya da Aliya wato umma, wacce suka hadu da ita a london taje karatu,coursemate dinsa ce,  suka qulla soyayyar su.Suna son junan su sosae hatta kai ma yanxu ana maganar aurensu.Bayan biki suma nn birnin tarayyar suka tare suka ci gaba da rayuwar su cikin kwanciyar hankali.Bayan haihuwar su na fari da shekara biyu neh mahaifan su Dr.Mahmud sukayi hatsari suka rasu a hanyarsu ta dawowa daga umra,, Allah ya jiqansu kowa yake cewa, dangi anyi kewarsu har an gode Allah,Mahmud da Khaleed sunyi kukan rashin iyaye ....Bayan anyi zama makokinsu an gama sae akayi rabon gado kowa aka basa nashi..



  KOMAI RINTSI.....馃槍


0鈨�3鈨�
   Bayan shekara 21

    Dr.Mahmud ya tsiri sake yin wani auren wanda shi yyi sanadiyyar samun sabanisa da haj.Aliya,, a yanxu yayansu uku neh babban Adam me shekara 23 sae Tasleem t biyo shi shekarunta 16 da dan dori sae dan auta wato jaleel shikuwa shekarunsa 9 neh....
     Bataso auren ba kou kadan wanda hakn yasa ta tusa yaranta tsanan matar uban.Koda yyi auren sunyi ta azabtar da ita kasancewar uban be cika zama a gida ba,danma momy nada hakuri dan koya dawo bata fada mishi abubuwan da ake mata,, a haka harta haifo yarta kyakyawar gske taci suna Aisha, sunan mahaifiyar momy ce..


     Fadwa ta taso bbu jituwa ko kadan a tsakaninta da yan uwanta,, tsakaninta dsu sai zgi da cin zali...kullum tana gun momyn ta a haka har Allah ya dau ran Dr.Mahmud fadwa nada shekaru uku da watanni ..mutuwarsa ta qara musu zaman takaici kunci, ya rasu ya bar momy da ciki 4mnths.


      Yanzu ya kaiga kou scul zasu saedae akaita da ban amma bazasu tafi da itaba ..kou a scul jaleel bsya so ace ita qanwarsa ce..Yana jss neh yanxu itakuma nursery1 take, bata ma jima da shiga ba dan bayan rasuwan babansu aka sata.Kwanannan faruk ya dawo daga uk yanda ya qare msters dinsa kan geology yanada 27yrs sae Tasleem dake nan apti tana karanta computer science tanada 21yrs.....

     Cigaban labari.....
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: KOMAI RINTSI....馃槍


          By
馃尫Hamagee馃尫馃摎馃摑


0鈨�4鈨�
Cigaba da labari...
A haka bacci barawo yyi awon gaba da momy a gefen Fadwa wacce ta jima da yin bacci saedae tana ajiyar zuciya jifa*2..


  Washegari da safe momy ta tashi tayi sallah ta yi musu breakfast sannan ta tada fadwa tayimata wanka itama tayi nata kasancewar yau monday neh momy zata sauqe ta a scul da kanta kwae sae ta wuce gun office dan yaxu ta fara aiki a ministry ov informatn...


   Tana ajiye ta a gate din makarantan sae ga wata yar yarinya itama dae bazata wuce shekarun Fadwan ba,Saeema kenan, qawar tace tare momyn saeeman ta shigar dasu sannan ta komo gun motar momy suka gaesa dan qawartace sunanta haj.Faty,tare sukayi secondary scul da jamia saedae ita bata qare ba kasancewar ita MBBS take, tana auren wani babban mutum dake aiki oil nd gas industrie  yayansu biyu kenan yanxun, Aliyu shine babba yana ss2 neh yanxu sae saeema ta biyun...


    Bayan sun gama yan hiransu sae kowa ta ja mota ta tafi..momy na zaune kan kujeran office dinta wanda yayi kyau iya kyau, yasha furnitures ga air-conditn,system neh a gabanta tana entering wasu documents amma da gani kasan tana cikin damuwa.....


     Shabiyu daedae ta ta fito ta kulle office din ta nufi parking space ta shiga mota ta kama hanyan zuwa daukan Fadwa,,12:23pm daedae ya mata a scul din saeta zauna jiran a tashesu dan 12:30 daman suke tashi kullum in banda fridy da ake tashinsu 12noon...

    Bayan sun tashi sae ta shiga ta daukota snnan suka nufa office din momyn dan daman bata tshi ba sae two take closing.A hanya naga ta staya ta shiga dan wani cafe ta siyo snacks da ice-cream sae youghurt da ruwa sannan suka wuce office din.Koda suka shiga ciki sae momy ta bama Fadwan wani cake da ice-cream 馃崷dan dama mutumin ta kenan,momy kuma ta dau youghurt da meatpie sae shawrma dan ita kyn zaqi basu dameta ba.Sukaci suka sha ruwa  Fadwa tayi ta ma wa momynta tadin uncle dinsu a scul har 2:00pm tayi sannan momy tayi closing ....


   Correction??09020364597 or whatsapp me 08102992472
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: *KOMAI RINTSI*......馃槍


  By 馃尫Hamagee馃尫

0鈨�5鈨�
   Suna isowa momy ta danna horn tym din aka bude ta shiga,parking naga tayi sannan ta fito Fadwa na biye da ita sukayi side dinsu suna shiga suka samu da wuta fadwa tazo kunna tv sae momy ta hanata tace sae tayi wanka tayi assingment dinta tukunna _Mommy yau baa bamu home work bafa_ ta fada kaman zatayi kuka, sae momyn tace eh ta bari sae tayi wanka haka ta hakura sanda tayi mata wankan itama tayi sannan ta dauro alwalan sallan laasar dan tayi azahar a office dama.Indomie kawae tayi musu bayan sun gma ci sae ta kunna mata kallon sannan ta wuce daki,,wani akin office ta cigaba da yi a system dinta kafin wayanta ya soma ringing,tana dagawa aka gaida ta ta ansa sannan naji tana cewa _Fadwa na palour tana kallo, ok tou Allah ya kiyaye hanya sae kin dawo_ sannan ta katse wayar..Faiza ce me aikin momy ta kira wayan....
    Karfe uku da minty arbain momy ta tashi tyi sallan laasar sannan ta kunna tvn dakinta tana kallo anan bacci ya dauke ta.Kaman a mafrki ta fara jiyo kukan fadwa aikuwa da sauri ta farka ta fito ko dankwali bbu aknta tana saukowa taga jallel da bulala yana ta tsalama fadwan ita kuma tana kuka ae da gudu tazo ta raba su tana tambayrsa _lfya meyasa yke dukan ta idan ta masa wani abunne bazae zo ya fada mata ba sae dai kwae yyi ta dukan yrinya kamar jakan gidan su_  ran momy be qara baci bama saeda ya fada mata abunda fadwan ta masa, wae uncle dinsu jallel dinne ya tambayeta ta san jaleel neh yaga surename dinsu daya sae tace mai yayanta neh shikuma uncle sae yazo yana tambayan jaleel din dama yana da sister a scul dinnan shine bsu zuwa tare yace mishi ae gidansu ba daya bane....Momy bata san lokacin da tace _shine don rashin imani zakazo kana dukanta ? Fice mun a daki mara mutunci_  yana fita yuuu sae side dinsu ya samu ummansu a daki ta idar da salla kenan tana kan sallayar,kuka ya fashe da umman ta soma tambayar shi meya faru yace _wae dan fadwa ta mun rashin kunya na buge ta shine ta  zazzagen  ta koreni a dakin_  yana kaiwa nan ya cigaba da kuka umma kuwa ta gama quluwa,ta tashi yuuuu sae side din momy tana huci....
    Momy kuwa bayan fitan jaleel ta jawo fadwa jikin ta duk ciwo yana jini ta soma lallaminta zuciyarta na quna saeda ta sake mata wanka ta dan danna mata raunikan da ruwan dumi sannan ta canza mata kaya ta kwantar ita ta tsura mata idanu......
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: *KOMAI RINTSI.....馃槍*

By 馃尫Hamageey馃尫

0鈨�6鈨�
   Jin qaran qofa neh ya katse momy da tunanin da takeyi,umma ce ta shigo tana ta ruwan bala'i da masifa _ina kike munafuka ki fito nan_ umma ke fadi.Da jin haka sae momy ta taso ta fito palourn yadda ta taradda umma nata fada tana jijjiga jiki da alaman dae jiran momyn takeyi ta fito..
     Tana saukowa ta ganta sae tace mata _lfya naganki haka?_ inji momy dan abun ya bata mamaki dan ita dae tasan ba wani abunda ya hada su da dadewa."Ban saniba munafuka"inji umma, ta fada ne a harziqe sannan ta cigaba da cewa _miye jaleel yayi miki zaki zage shi ki kore shi shida gidan uban sa_? Sae momy tace _ni ban zage shi ba illa dae na masa fada dan abunda yyi be dace ba, ina kwance fa a daki naji kukan fadwa shine na fito dan ganin ko meke faruwa kwae sae na ganshi da bulala yana zaneta shine na raba su, yanxu fadwa harta kai na duka da bulala, kuma idan ta mishi abune ba sae ya fada mun ba balle ma bbu abunda ta mishi wae dan...._ bata qarasa ba umma ta cigaba _tayi mishi rashin kunyan sannan kice bata mishi komae ba, to wllhy zan dau mataki akanki keda yar ki_ sannan ta fice ta banko kofar da qarfi wanda yasa fadwa tashi daga baccinta....
   Tana fita tayi side dinta ta samu jaleel na palour kan kujera har yanzu kuka yakeyi ta zauna a gefensa tana lallaminsa _kayi hkuri kaji autana in ta sake maka wani abu ka mata dukan tsiya nina baka wannan izinin kuma idan uwarta ta maka wani abun kazo ka gaya mun_ yace _tou_ yana share hawayen idonsa... tasleem ce ta shigo da sallamarta umma ta ansa sannan ta zauna kan daya daga kujerun palourn ta kalli umma da jaleel sannan tace _umma meyasama autanna ki ne _? Umma tace _wae fadwa tayi mishi rashin kunya danya buge uwarta ta zage shi ta koresa_ Tasleem ta yamutse fuska tace _lallae yaro da gidan ubansa ai da ka mata rashin mutunci_ sae umman tace _barni da ita kwae yanzuma na sameta na kashe mata warning ae_

    Gurin momy kuwa daki ta koma yanda ta taradda fadwa ta tashi amma tana kwance jikinta duk yyi zafi zazzabine ya kamata,haka ta dauketa ta kaita asibiti,bayan wasu yan gwaje2* magunguna aka rubuta musu,  koda likitan ya tambaya wa yyi mata bugu hka sae momy tayi karyan cewa a a scul neh sae kwae yace Allah ya kiyaye gaba amma wannan ae bata kai na duka hka ba,dan Allah a ringa kula momy tace insha Allah sannan tayi godiya suka tafi bayan ya rubuta musu wasu magungunan dan ciwukan jikinta,,bayan sun siya sae suka wuce gida....
   Washegari ya kasance ranar talata neh fadwa bataje scul ba saboda yanayin jikin nata,, around 10:13am sae momy taji sallamar Faiza dama yau tace zata dawo amma momy tayi mamkin ganinta yanxu dan ta mayar saeda yamma zata dawo,ta ansa sallamar gami da jin dadin ganinta a yanxu dan da batazo yanzunba da saedae momy ta fasa zuwa aikinta...
   Bayan sun gaisa sae faiza ke tambyan momy lfya fadwa bata je makaranta ba sae momy ta fada batada lfya sannan ta koro mata duk abubuwan da sukayi ta faruwa bayan tafiyanta daman tasan duk abubuwan dake faruwa a gidan tace _tou Allah ya kauta_ momy tace "ameen" sannan ta tashi shirya dama tayi wanka sannan ta tafi office dinta.....

For comment whatsapp me @ 08102992472
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: *KOMAI RINTSI...馃槍*

*By* 馃尫Hamergee馃尫


0鈨�7鈨�
    Koda momy ta tafi hankalin ta kwance yake bata tunanin komai dan tasan indai faiza na nan tou kaman tana nan neh dan zata kula mata da fadwa da gidan kaman tana nan.Bayan momy ta fita faiza ta gyara gidan tsaf duk da dai ba wae datti yyi ba,bayan ta gama sae ta iza girkin rana sannan fadwa ta tashi daga bacci,, wanka tayi mata sannan ta bata abinci taci sae ta bata maganinta da momy ta bari a bata, bayan sun gama around 12:35am  sae suka zauna kallo a palour.Ba laifi jikin fadwa ya danyi sauqi dan har tadi takeyiwa faiza...
    Kamar kullum past two momy ta dawo taci abinci tyi wanka sannan bayan sallan laasar suka shirya suka je kasuwa sayen kayan abinci sannan suka wuce wani babban shoppng mall suka gama siyayyansu suka koma gida.....Washegari fadwa taje scul dan ta samu sauqi ssae,hka rayuwa ta ci gaba musu basu sake samun wata matsala da su umma ba...

  *5 months l8re*....
   Yau ya kasance ranar friday,12noon momy ta taso daga office, tun tashinta take jinta baa daedae ba dauriya kwae takeyi,bayan ta tashi ta dauko fadwa a scul sae suka dawo gida, wanka tayi da qyar ta hado da alwala sae tayi sallah,koda faiza ta kawo mata abinci cewa tayi ta tafida shi kwae bata ciba,, faiza ta tambyeta kou bata jin ddi neh tace mata _ehh_.....Tana nan a kwance a qasa yadda tayi sallahn saeta fara jin kaman ana mitsininta a ciki sae qaruwa kuma yake,, ciwon ciki da baya neh suka sata a gaba lokaci guda _Faizaaa,faizaaaa, faiz......_ bata gama fada ba sae taji ta kasa,, da sauri faiza ta shigo dakin dan dama a saman take dakin fadwa ita kanma bacci takeyi

_______________
   Tana shigo ta fita ganin halinda momyn take ciki  drivern su taje tayi ma magana da sauri ta taimaka ma momy suka shiga motan sannan suka nufi asibiti.Suna isa aka karbesu da gaggawa aka dauko wheel-chair aka tura momy sae labour room yadda ta haifo kyakyawan danta me kama da fadwa..

  For comment whatsapp me @ 08102992472...
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: *KOMAI RINTSI....馃槍*

*By*馃尫Hamergee馃尫

0鈨�8鈨nd0鈨�9鈨�
   Haj.Aisha ce keta safa da marwa a ward din daedae nan nurse din da ta karba haihuwar ta fito,tana kallonta ta nufo ta da sauri nurse din ce ta tambayeta _kuna tareda wacce ta haihun neh?_ haj.aisha ta ansa da _eh, ta sauka lfya?_ nurse din tace _lfya klou kuna iya shiga ku ganta a can dakin ma_  dan a lokacin faiza ma ta shigo taje gida dauko kayan baby dana momy da fadwa kamar yadda haj.aisha ta umurceta da tayi...
 Nurse din na tafe suna binta har zuwa dakin ba nisa da inda suke,suna shiga sukaga baby da momy ita kanma bacci neh ya dauketa,faiza ta dauki babyn tana kallo kafin ta miqowa hajiyan momy,,Abba wato mahaifin momy neh ya shigo dakin gami da sallama bayan ya tambyi wata nurse dakin ta nuna mishi,suka ansa bayan ya shigo faiza ta gaida shi ya ansa da faraa sannan ya juya yana yima babyn wasa sae ya juya yana kallon hjiyan yace_kin sama mata wacce zatana kulada ita neh kou kuma zakije da kanki?_ tace _ai da cewa nayi zamu tafi gida kwae da ita inaga kaman zaefi sauqi._  Abba yace _aa ta koma gidanta kwae sae daga baya ta dawo ko bayan anyi suna kafinnan ma mu tattauna da yan iyayen mijin natan_ haj tace! _tou shikenan sae ta koma tunda ga faiza,inyaso sae na ringa dubasu tym to tym_  yace _da  yafi, yanxun an kirasu an sanar da su ta hauhu neh?_ hajya tace _eh,na kira ita matar gidan sun dae na sanarda ita amma bata zo ba har yanxu_ yace _tou ba laifi_ sannan ya fice..
   Bayan sallahn ishai suka tattara kayansu bayan momy ta tashi a bacci sae suka koma gida,momy tayi wanka da taimakon hjya snnan fa'iza tayima bbyn itama.Sanda dare ya soma yi kafinnan hjiyan ta tafi..*hka suka cigaba dayi hjya na zuwa lokaci lokaci tana dubasu faiza kuma na rainon baby kuma tana timakon momy har ran suna,,ana gobe suna gidan wan babansu fadwn suka zo wato Brrs.Khaleed,shi ya rada ma yaron suna.Yaron yasha sunan kakanshi (baban momy),wato Usman sae ana kiransa da khalifa.Ansha suna an watse dangin momy dana baban fadwa duk sunzo,na nesa dana kusa....
    2day ltr..
Alhj Usman da wan baban fadwa da kuma wasu baffanunsa suka zauna sukayi magana kan yanxu kam momy zata iya komawa gida tunda ta gama idda.Fadwa kuma zaa barta gun yan uwanta sae momyn ta tafi babyn,a haka suka tsaida magana sannan kowa ya koma gidansa, momy ta koma gida amma fadwa na gidansu faiza ma ta tafi dan ba abunda zata zaunayi.....
  Da kyar umma ta yarda zata zauna da fadwa dan a cewarta bazata yi raino ba...

    Kar kuji ni shiru da yawa bana jin dadi neh amma in na samu sauqi komi zae canza insha Allah馃檹馃徎

  For comment whatsapp me @ 08102992472 or contact me @ 08091045865
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: 馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁 *KOMAI RINTSI.....* 馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯

_Written by_ 馃尫Hama gee鉁嶐煆�

Page 馃敓
    Rayuwar qunci, kadaeci bbu wanda Fadwa bata saba dashi ba a yanxu,, ta sauya yanxu kaman ba itaba baa kulawa da ita kwakwata ko wanka sae dai in tayi niyya tayi da kanta randa batayi wannan tunanin ba kuwa sae dai ta zauna haka dan umma tace ita baza ta iya rainon yar kishiya ba...kullun da datti take zuwa scul dan yanxu sun koma tana nursery2 yayanta jaleel kuma ya shiga js 2....
     Kullum a scul sae haj.faty wato (maman saeema qawar momy) ta bata abun break tareda yi mata dadadan kalamai kan tayi hakuri in ta gama class din da take yanxu zatazo ta dauke ta ta koma gidansu wajen saeema, idan fadwa taji haka sae ta dan ji dadi (abunka ta yarinta) da haka suke rabuwa da ita, idan an tashi kuma fadwa na riga tafiya dake ana riga zuwa daukansu,ranan da tsiyan jaleel ya tashi kuwa cewa yakeyi shi dae ba zae tafi da ita ba saedae akai shi a dawo a dauketa kuma hakan akeyi,infact ya sha yin hakan (ranan da suke tashi tare kenan)...islamiyan su kusa da gida neh wannan tana iya zuwa da kanta.
    Momy fah?
kullum tunanin momy a wane hali fadwa ke ciki? Da tunanin take tashi take kwana (Allah sarki,uwa kenan鈽�),, ranan da haj.faty tazo gun momy neh take fada mata halin da fadwa ke ciki kuma tana yawan yin kuka in sun hadu wae ta kaita kun momynta....
[2:54pm, 12/5/2016] Hamagee馃尫: 馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁 *KOMAI RINTSI* 馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯馃崁馃尯

_Written by_ 馃尫Hama gee鉁嶐煆�

Saturday 27 October 2018

Hausa Novel: Agola ( By Nabila Rabiu Zango )

October 27, 2018 0


🙆🏻  AGOLAH!!!nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABIU ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ (H,O,N,A)
   
SADAUKARWA!!!
 Zuwaga dukkanin yan uwa da abokan arziki, ina me nuna farincikina gareku, Allah yabar zumunci, ameen.

Bismillahir Rahmanirrahim.

Part 1.....5

Agarin kaduna, cikin unguwar Sarki. Awani katon gida, nashiga domin dauko maku labarin cikin gidan.
    Alhaji Abba Bala, hamshakin me kudine, yanada mata daya da ya,ya biyu mata, Sunan matarshi Hajiya Zarah, takasance yar garin zariya, diyace agurin Malam Garba da matarshi Asabe, kishiyar mamanta, ce, tana kiranta da inna, Asabe takasance mace me kissa, hakan yasa take zaune da Zarah tamkar ita ta haifeta, babu wanda yasan dalilinta nayin haka, talakawa ne acikin danginsu kaf Zarah ce kadai tayi sa,ar auran me kudi, dalilin haduwarsu kuwa lokacin da Alhaji Abba yaje zariya acikin unguwarsu Zarah, yaziyarci wani abokinshi, ahanyarshi ta dawowa yahadu da Zarah tadawo daga aiken da Innarta tayi mata, lokaci guda yaji yakamu da sonta, ahaka. Bayan sungaisa yanemi data nuna mashi gidansu, yayi mata godiya yatafi.

Tundaga ranar soyayya tashiga tsakaninsu, kai tsaye yanemi izinin aurenta agurin mahaifinta, babu bata lokaci ya amshi bukatarshi.
Zarah Allah yayi mata son kudi, babu abinda ta tsana irin talaka, duk da Allah yayita acikinsu amma bata son su, ko taron danginsu akeyi bata shiga, hatta da iyayenta hakuri sukeyi da ita, tasha yin mafarkin ta auri me kudi, segashi Allah ya amsa mata addu,arta tasamu me kudin,
   Zarah bata damu da ilimin addini ba, ko sallah bata damu dayiba, amma tunda suka hadu da Alh, Abba taboye duk wani halinta marar kyau, shi kuma duk farin ciki ya isheshi yasamu diyar gidan mutunci, duk da azahiri iyayenta suna da mutunci amma bata gado suba.

Ahaka akayi aurensu, aka kaita kaduna cikin unguwar sarki akaton gidanta, haka suka cigaba da rayuwarsu cike da so da kauna, hankalinta ya kwanta, arzikin mijinta se karuwa yakeyi, hutu ya zauna mata tuni fatarta, ta murje tayi kyau sosai, tuni ta manta da iyayenta da danginta, tunda akayi bikin bata zuwa garinsu sosai, sede idan mijinta ya matsa mata, shima sede suje tare kuma bazata kwana ba, ko bikin dangine bata cika zuwa ba,  idan ma yabata kudin gudummuwa ko kwatar abunda yabada bata basu, gashi Allah yayi mata rowa.

Ahaka ta haifa mashi diyarta ta farko me suna Hauwa,u sunan mahaifiyarshice yasa dan duk iyayenshi sunrasu, dama shi kadai suka haifa, sede danginshi, hakan yasa aka sama diyarshi sunan mamanshi, ana kiranta da JIDDAH.

Bayan sunanta ne Alhaji Abba yabama Zarah kudi masu yawa yace tafara bussiness, kuma shine yayi mata jagora zuwa dubai domin fara kasuwanci, daga haka harta fara zuwa ita kadai, ahaka ne tahadu da wata mata me suna Hajiya Karima, itama babbar yar kasuwace, halinsu ne yazo daya dan danan suka kulla kawance, itama anan kaduna take. Kawancensu sukeyi sosai, Karima takara nuna ma Zarah duniya anan idonta yakara budewa takara koyon duk wata kissa, sede ita karima bata bin bokaye sede duk wata kissa ta iyata, shiyasa Zarah take zaune da mijinta lafiya, tana yimashi biyayya, saboda yana sakar mata duniya, ita kuma babu abinda takeso kamar kudi, tun bayan haihuwar Jidda taso tayi planing amma Karima tahana ta, acewarta tabari tahaifi namiji.

Bayan shekara biyu da haihuwar Jidda takara haihuwar diyarta mace, har kuka seda tayi, saboda bata samu namiji ba. Ranar suna yarinya taci sunan maman Zarah Saratu, ana kiranta da JALILA.
   Tun daga lokaci Karima tarakata aka tsaida haihuwar acewarta karta tsufa dawuri. Haka yara suka taso cike da kulawa, sudukansu suna da kyau, sede Jalila tafi Jidda kyau, Ahaka suka shiga makaranta, Jidda na P. 1 aka saka Jalila, haka suka cigaba da karatunsu, harsuka girma, alokacin Jidda tana da shekara 18 Jalila tanada 16, alokacin Jidda tana ss 3, Jalila tana ss 1. Halinsu kwata kwata bezo daya ba, Jidda gab daya irin halin Umminsu tadauko, Jalila kuwa irin Halin Dadynsu gareta, tunda suka gama Primary Jidda tafita daga islamiyya, Jalila ce kadai take zuwa, sede Dadynsu besan bata zuwa ba, kasan cewar aiyuka sun mashi yawa, ga tafiye tafiye dayakeyi. Ita kuma umminsu bata damu da ilimin addini ba. Tun Jidda tana ss 1 tafara kula samari, duk wanda zekirata yabata kudi to zata iya binshi duk inda yace, so dayawa Jalila tana kawo kararta amma Umminsu bata daukar maganarta abakin komai, karshema sede takoreta, ahaka harta shiga ss3 alokacin tahadu da kawaye yan duniya tuni suka maida bin maza aikinsu, sede kawarta. Ameera tafisu duniyanci, hakan yasa takaisu asibiti domin suma ayimasu planing. Tun daga lokacin suke sheke ayarsu, kudi suke samu sosai, dayake Jidda tana bama Umminsu kudi hakan yasa tarufe mata baki, takuma zama yar gaban goshinta. Kullum Jalila setayi kuka idan taga halin da yayarta tasa kanta, amma sanin kotayi magana babu wanda ze kulata yasa tayi shiru , saboda Zarah taja mata kunne akan idan har tafada ma Dadynsu wata magana akan Jidda seta tsine mata. Addu,a kawai takeyi mata, sannan ta maida hankalinta akan karatunta na boko dana islamiyya.

Alh. Abba ne yafito cikin shirinshi na tafiya sokkoto. Matarshi da yaranshi biyu, suka rakoshi har bakin mota. Alh, yace to Hajiya nizantafi akula da gida, insha Allah gobe zandawo, kallon yaranshi yayi yace ku kula da karatunku ina fatan babu wata matsala ko? Jidda tayi saurin fadin dady kayan kwalliyarmu sun kare, dariya yayi yace toga dubu 20 nan ai sun isa ko? Karba tayi tana dariya, Jalila tace dady mungode Allah yakara budi. Allah yatsare hanya, sosai yakejin dadin addu,ar da Jalila takeyi mashi aduk sanda yatashi yin tafiya, ita kuwa Jidda tuni tajuya tanufi gida tana murnar samun kudi, daga nesa take fadin dady seka dawo ayo mana tsaraba. Murmushi yayi ya girgiza kanshi yace toni zan wuce, Zarah ta rungumeshi tana fadin seka dawo mijina, Ganin haka yasa Jalila tayi mashi sallam itama ta juya, kiss yayi mata agoshinta yana kara rungumeta, anan yakara mata bandir guda na 1k yace kozata nemi wani abu kafin yadawo. Godiya tayi mashi sannan yashiga motarshi yawuce.

Dayake tafiyar batayi mashi sauri ba, kasancewar tsaye tsaye dayayi kuma dama befito gida dawuru ba, hakan yasa beshiga sokkoto dawuriba segurin karfe 8 na dare, kaitsaye yawuce gurin wadda yazo, dan agobe yakeso yakoma, shiyasa seda yaje yagama abinda yakawoshi sannan yawuce masaukinshi, misalin karfe 9: 30, dayake awajen gari masaukin nashi yake, yafito daga cikin gari tun daga nesa yaga kamar ana tsaidashi, sede beda niyar tsayawa, dan yasan halin yan, fashi babu abinda basayi inde suna son sutareka, haryawuce yaga kamar mata guda biyu ne abikin titin wadanda suke tsaidashi, gani yayi sunata waigen bayansu gashi daya daga cikinsu ta tsugunna kasa kamar tana kuka ganin yawucesu.
    Cikin sauri ya taka burki yakoma baya, suna ganin ya tsaya da gudu daya takama hannun dayar suka nufi gurinshi, tambayarsu yafarayi, amma cike dasauri suka bude bayan motar suka shige. Dakyar take magana, dan Allah bawan Allah katemakemu kayi nisa damu daga gurin nan, wlh sunbiyo mu zasu kashemu...... Ai dajin haka yatada mota yafisgeta suka bar gurin, lokacin damasu binsu suka iso ko alamarsu basu gani ba, haka sukaita dube dubensu, ganin dare nayi suka juya domin komawa gurin Ogansu.

Urs
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/6, 6:12 AM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻 AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Part 5.....10

 Parking yayi adede wani karamin gida, inda yakasance masauki agareshi aduk lokacin dayazo sakkoto, fita yayi suma suka, fito, tsayawa sukayi suna kallonshi, ahankali yace bansan ina zan kaiku ba, kuma gashi dare yayi, duk da kunce infitar daku wajen gari, agaskiya bazan iya kaiku ba, saboda dare yayi kuma gashi ku mata ne, idan harkun yarda dani kushigo ciki ku kwana idan Allah ya kaimu gobe semusan abinyi, domin nima ba,a garin nan nake ba, wani aiki yakawoni yau, kuma nagama gobe zankoma kaduna acan nake da iyalina.

Kallonshi babbar ciki tayi nawani lokaci sannan tace bakomai munyarda da kai. Bude masu gidan yayi bayan sunshiga yakoma yakwaso kayan cikin motar daya siyo, yashigo ya kulle gidan, zaune suke afalo, shima zama yayi sannan yace. Ga dukkan alamu kuna dauke da yunwa, sede abinci beda yawa kaza ce da lemu nasiyo se biredi, kucinye kawai gobe idan nafita nasamo mana abinda zamu karya dashi, matar tace mungode sosai, amma yanzu abinda kedamuna bamuyi sallar magriba da isha,i ba, murmushi yayi yajinjina irin addini na wannan matar, daganinsu kasan suna tare da yunwa, amma duk da haka take maganar sallah.
      Dakinshi ya nuna masu yace akwai bandaki aciki idan sungama ga abin sallah nan, bayan sunshiga shi kuma yazauna afalo yana tunaninsu, yakosa sugama abinda sukeyi ya tambayesu labarinsu.

Babbar matar takalli yarinyar dasuke tare, da alama diyarta ce saboda tsanin kamar dasukeyi, tace kishiga ciki kiyi wanka sannan kiyo alwala, zama tayi tajirata, har tagama tafito sanye da kayan data cire, daukar hijabinta tayi ta kabbara sallah,ita kuma uwar tashiga domin yin wanka.

     Motsi yaji yasashi saurin dagowa, ganinsu yayi sunfito tsaf dasu, anan take ya iya hango kyawun dake tare dasu, duk da akwai alamun walaha atare dasu hakan be hana kyawunsu fitowa ba, musamman dasukayi wanka suka fita daga cikin dattin dasuke, duk da basu canja kaya ba.

Abinci yadauko masu yamika masu lemu da ruwa harda biredin, murmushi babbar tayi tace da alama kaima bakaci komai ba, kuma gashi kabamu duka, kadebi kazar semu hada biredin, yace a,a kude kuci ku koshi tace Allah bazamu iya cinyewa ba, bata jira abinda zece ba, ta deba mashi kazar dan tana da girma ta mika mashi da biredin, amsa yayi yana mata godiya, murmushi kawai tayi takoma kusa da diyarta suka fara cin tasu, shide ci kawai yakeyi amma hankalinshi yana kan wannan matar, addu,a kawai yakeyi acikin ranshi Allah yasa bata da miji, dan tunda tafito yaji wani irin yanayi akanta.

Bayan sungama takwashe kayan tasa aleda ta kaisu cikin dustbin tasaka, kalon diyarta tayi taga tana gyangyadi, Alh, yace yan mata bacci kikeji kije ki kwanta, murmushi tayi tace to Dady, sosai yaji dadin yanda takirashi da dady, tashi tayi tamasu seda safe tashige daki, matar tace Alhaji kai kuma a ina zaka kwana? Murmushi yayi yace bakomai anan ma ya isheni, zama tayi akasa tayi kasa da kanta tana wasa da yatsunta.

Shima kasa yasauko dan nesa da ita kadan, yace duk da bansan sunanku ba, daga ke har diyarki kiyi hakuri kifadamun labarinku dan bazan iyayin bacci ba idan har banji dalilin dayasa akeso akasheku ba. Idan har babu damuwa inasonjin labarinku, dan Allah.

Hawayen dake idonta ta goge tace tabbas Alhaji ka cancanci kaji labarinmu, domin katemakemu kuma nayarda da kai.
    Nide sunana HAJARA amma anfi kirana da HAJJO kasancewar mudin fulanine, Wannan kuma diyata ce sunanta FALAK, kuma ita kadai Allah yabani, mijina Allah yayi mashi rasuwa yau wata 5 kenan. Ajiyar zuciya yayi aranshi yana fadin Alhamdulillah.

Asalin labarin HAJJO...............
    Ita kadai Allah yabama iyayenta, kuma su fulanin daji ne, basu da taka maiman garin zama, ako da yaushe suna. Canza gurin zama daga wannan guri zuwa wannan, tun bayan auren Baffanta da Innarta suka bar garinsu wanda yake acikin niger, dan sunkasance fulanin niger, haka suka rika yawo gari gari tare da Shanunsu, duk inda sukaje sukan kafa bukkarsu agurin suzauna har zuwa wani lokaci, idan sun gama sesu tashi zuwa wani gari, acikin haka har suka haifi Hajjo, wanda sunan innar Baffantane aka samata.

Lokacin da Hajjo tayi girma har takai sheakara 10 alokacin suka yada Zango acikin garin gusau, acan bayan gari suka kafa bukkarsu tare da wasu yan uwansu fulani dasuka hadu ahanya, koda sukaje gurin sunsami fulani dayawa agurin, anan Baffa yaji dadi, dan tunda suke yawo basu taba haduwa da fulani dayawa kamar wannan ba, anan suka zauna suka cigaba da kiwonsu, inda Inna yakeyin fura da nono tana dora ma Hajjo tana bin sauran sa,anninta zuwa cikin gari sukai talla.
      Baffa dakanshi yayi sha,awar saka Hajjo makarantar boko kasancewar yaga wasu daga cikin yaran gurinsu suna zuwa, ahaka wani abokinshi jauro yayi mashi jagora zuwa makarantar da diyarshi take, shima yasaka Hajjo.

    Haka rayuwarsu tacigaba da tafiya gwanin dadi, su Hajjo suna zuwa makaranta, ranar da babu karatu kuma sutafi cikin gari talla.

Ahaka harsuka gama primary alokacin Hajjo tana da shekara 16, kyawunta yakara fitowa sosai, kowa sonta yakeyi, watarana suntafi kasuwa ita da kawayenta domin aranar kasuwa takeci, sunje kai talla
    Tunda sukaje kasuwar ta lura dawani yanata kallonta, ahaka harsuka saida suka siyi abinda zasu siya suna shirin tafiya gida. Sallama taji anyi mata, amsawa tayi tare da juyawa domin ganin me mata sallama, wannan wanda tagani yana kallonta shine de tare da abokinshi.

Sannunku yanmata yace yana kallonta fuskarshi dauke da murmushi, bayan sun gaisa yake tambayarta sunanta, tace Hajjo, murmushi yayi yace Hajara kenan, amma sunan akwai dadi, ni sunana Bashir, kuma ni dan sakkoto ne, ina zuwa nan duk ranar kasuwa, amma Allah betaba jadamu ba, se yau, murmushi tayi tace zanwuce abokan tafiyana suna kirana kada dare yayi, kallon abokinshi yayi yace to abokina nima tafiya zanyi dan banason dare yayi saboda barayin hanya, dan Allah kabisu Hajjo kaganemun gidansu idan nadawo sati mezuwa kwana zanyi seka rakani. Godiya yayi masu sukayi sallama.

Tundaga wannan lokacin soyayya tashiga tsakanin Bashir da Hajjo, har iyayenta sun san dashi,  Baffane yace ma Hajjo idan Bashir yazo yanason ganinshi.

    Zaune suke abisa tabarma, anan Baffa yake tambayar Bashir asalinshi, Yace nide sunana Bashir, kuma ni dan asalin sakkoto ne, iyayena sun rasu tun ina dan shekara 20, banida kowa se kawuna, agurinshi nake kuma gida daya muke dashi, kasuwanci shine sana,ata ina zuwa garuruwa kasuwanci, kuma a sakkoto gidana yake wanda mahaifina ya mutu yabarmun.
    Baffa yace Alhamdulillahi, anan shima yafadamashi alabarinsu, sannan yace tunda naganka naji hankalina ya kwanta da kai, kuma nabaka Hajjo, ko yaushe kake so adaura maku aure zaka iya zuwa, sede inaso dan Allah karike mana Hajjo bisa gaskiya da amana, ita kadai Allah yabamu, kuma kaga bamuda kowa anan, gashi ba gari daya zamu zauna ba, kasan mudin makiyaya ne, inaso karike mani ita, kuma dan Allah karika kawo mana ita duk sanda zaka zo kasuwa, kafin mutashi daga nan, duk da gaskiya bayanzu zamu tashi ba, dan naji dadin zaman gurin nan.

Bashir yace insha Allahu Baffa zaka sameni me riko da amanar daka bani, kuma insha Allah sati mezuwa tare da kawuna zamuzo se adaura mana aure, banaso ku wahalar da kanku, Hajjo kadai nake so, saboda haka kada kusiyi komai. Godiya Baffa yayi mashi sannan yatashi yakira mashi Hajjo.


Bayan sati guda Bashir yazo da kawunshi Wanda yake kanin mahaifinshi dasuke uba daya, sunanshi Lado, amma mutanan gari suna kiranshi da Figo. Kasancewarshi cikenken dan duniya, danshi haryanzu beyi aure ba,sede lalata yaran gari, beda wata sana,ar data wuce shaye shaye da sata, shine oga acikin group dinsu, dan har yara gareshi. Bashir hakuri kawai yake dashi, tunda agida daya suke, sede shi kawu Figo adayan part din yake.

Bayan andaura aure aka shirya Hajjo cikin dinkunan da Bashir yakawo mata, sosai tayi kyau ahaka sukayi sallama da iyayenta suna kuka tafito, kawayenta suka rakota, harbakin mota suka kaita, suma kukan sukeyi ahaka suka tafi, ita kada abaya Bashir da kawu agaba, Bashir ke tuka motar. Tunda Kawu yaganta yake hadiye miyau yana murmushi aranshi yana fadin tsuntsu daga sama gasashshe.

Bayan sunje gida ya aje kawu sukuma suka shige gidan, gidan yayi kyau sosai, komai yasaka aciki kayan more rayuwa masu kyau yasa mata.

Ahaka sukaji gaba da rayuwarsu cike da so da kauna, komai najin dadi Bashir yanayi mata, sosai yake taka tsan tsan da gidanshi, saboda kawu, dan yafikowa sanin halinshi, ko abincin da Hajjo take bashi be bari takai mashi shine yake bashi da kanshi, idan kuma tafiya takamashi sede yakai Hajjo gidan abokinshi Saddik ta kwana, duk yanda kawu yaso kebewa da Hajjo Bashir yahana, idan yashigo gidan sede idan Bashir yana nan. Duk sanda zeje gusau cin kasuwa tare da Hajjo yake zuwa, sosai Hajjo tayi kyau, takara girma.

Bayan shekara biyu da aurensu tahaifi diyarta me kama da ita sede Allah yayima yarinyar kyau sosai, tun tana jaririya, ranar suna Bashir yasa mata FALAK, dan yace yana son sunan sosai.

Tunda FALAK ta girma yasata a primary, ranar dazeje gusau tare suka tafi, kwnansu 2 sannan sukafara shirin dawowa, Inna tadauko wasu awarwaro masu kyau guda biyu ta bama Falak, kasancewar sun mata yawa yasa Hajjo ta amsa tasaka a hannunta, haka taji kamar karsu tafi, Baffa yakara tunama Bashir akan rikon amanar daya bashi, haka sukayi sallama suka tafi.

Urs,
NABILA RABI,U ZANGO
( Nabeelert Lady)
08028525263
[7/6, 1:17 PM] YAYA HAYAT: 🙆🏻😭😭🙆🏻AGOLAH!!!Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI,U ZANGO
(Nabeelert Lady)

@ ( H,O,N,A)

Tuesday 23 October 2018

Hausa Novel: Shi Kadai Nake So ( By Beelybadaru )

October 23, 2018 0




*SHI KADAI NAKE SO*
🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟
           ✨✨✨
              ✨✨
                 ✨

✨By Beelybadaru😍✨

_Bismillahir-rahmanir-rahim_

*Wannan littafin nawa qagaggen labari ne banyi don cin xarafin wani ko wata ba, idan yayi dai dai da labarin rayuwarka ka gafarceni, kuma kar wanda ya juya min labarina ta wata siga, wanda yayi hkn na barsa da Allah...*


            ✨1 to 5✨

_I dedicated this page 2 u Ayusher Moh'd, Rabi'at sk msh, Asy khaleel, Wally, Aneelurv(Sweet dota), First lady, Mufeeda Mu'axu, HummyB(Melody), Afma, Yarruma(Sweet momma)._


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

```Kallon juna suke cike da so da qauna, kai da ka gansu xaka tabbatar da cewa su masoyan juna ne na ainihi. Ita ta soma sauke idonta daga kallon da suke ma junansu, sannan ta dago tare da cewa "*Habeeby* ina sonka fiye da yanda nake son kaina, bana tunanin xan iya rayuwa ba tare da kai ba, kaine majinginin rayuwata idan ka matsa rayuwata gaba daya rugujewa xatayi".

Dagowa yayi shima ya kalleta cikin so da qaunarta da suke yawo cikin jinin jikinsa sannan yace "*Habeebty* sonki a cikin jinin jikina yake, soyayyarki wani bangarene mai mahimmanci a rayuwata, cireshi a cikin xuciyata abu ne mai wahalar gaske, ta yaya kike tunanin xan iya rayuwa babu jini a jikina? Ta yaya kike tunanin xan iya rayuwa babu xuciya a jikina? Cire sonki a raina ba abune mai yuwuwa ba, don kuwa idan har aka ce xa'a cireshi ai dai a debe duka jinin jikina domin kuwa sonki a cikin jinin jikina yake yawo".

Lumshe ido ta tayi cike da jin dadin kalamansa, haqiqa sunyi nisa a soyayyar junansu, rabasu abune mai wahalar gaske.

Bude baki tayi da nufin yin magana sai ji tayi an fincikota ta baya, waigawa tayi da sauri don ganin ko waye, gabanta ya fadi ganin Abbanta da tayi tsaye a gabanta fuskarsa daure kamar wanda aka aikoma da saqon mutuwa.

Jikinta ne ya dauki kyarma, durqushewa tayi a gabansa hawaye har sun soma xarya a kumatunta, shima durqushewar yayi cike da jin tsoron abinda Abba xaiyi masu.

Wani wawan mari Abba ya watsa mata, a gigice ta dafe kuncinta don har wasu taurari ta gani shima da hanxari ya dafe kuncinshi don ji yayi kamar shi aka mara don yaji xafin marin har cikin xuciyarshi.

Cikin bacin rai Abba yace "*KHADEEJAH* ni xaki maida qaramin mutum? Ni xaki kunyata? Ke har kin isa in yanke magana a kanki ki bijiremin? To bari kiji in fada maki ko xaki mutu baxaki auri wannan yaron ba auren xumunci xakiyi kamar yanda kowane dan'uwanki yake yi".

Ya waiga ya kalli saurayin da har lokacin bai sauke hannunshi  daga dafe kuncin da yayi ba, yace " Kai kuma ban gargadeka ba akan kar na sake ganinka da diyata ba? Karka kuskura na sake ganinka da ita idan ka bari hakan ta faru......" Yayi kwafa, sannan ya juya ya fara tafiya can ya waigo kuma ya kallesu sannan yace "Ki tabbatar da kin shigo gida cikin secon biyu".

 Da sauri ta miqe ta qarasa gabanshi ta durqusa tare da hade hannayenta biyu guri guda sannan cikin muryar kuka tace " Abbana na roqeka da Allah kayi hkr kayi min rai karka rabani da *AHMAD* wllh shine rayuwata baxan iya auren kowa b in bashi ba, *SHI KADAI NAKE SO* zuciyata tarwatsewa xatayi Abba idan har ka rabani dashi".

Wani dogon tsaki yaja ya tare da yin ball da ita yace "Ah lallai dole xakizo ki tasani ki ri qa gayamin magana n ranki, to bari kiji in gaya miki dolenki ki amshi auren xumunci kamar ynd yan uwanki suka amsa, daga rana irin ta yau bake ba Ahmad kinji na fada miki".

Jin hakan yasa Ahmad yayi saurin qarasowa wajen Abban shima ya durqusa gabanshi tare da cewa " Abba don Allah karka rabani da Khadeejah wllh *ITA KADAI NAKE SO* Abba meyasa kake neman ruguxa mana rayuwarmu, Abba don Allah kayi hkr ka barmu  mu auri junanmu".

Banxan kallo ya watsa mashi sannan ya shige cikin gida. Ahmad har ya fara xubar da hawaye, da sauri Khadeejah tace "Ka daina xubar da Hawayenka Habeeby, xuciyata quna take a duk sanda naga hawayenka na xuba".

Shima kallonta yayi sannan yace " Habeebty kema ki daina xubar da naki hawayen ko kadan bana son ganin hawayen


Monday 22 October 2018

Hausa Novel: Zuciyarmu Daya ( By Eshat )

October 22, 2018 0




 *_ZUCIYARMU 'DAYA_ .*

漏Mamuh geee


For you my *zinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem._

1-2

Zaune take Bakin gadon da abbanta ke kwance yana jinya tsawon shekara biyu.
Hawaye ne kwance a fuskarta wa'inda zubowarsu sun zame mata azaliya.

Shekarar abbanta biyu a kwance rigis yana jinya,
Ita ke jinyarsa,ita ke aikin Samar da abibda zasuci duk da qananun shekarunta da basu haura sha bakwai ba.

Kallon 'dakin dasuke ciki tayi
Babu komai aciki banda ru6a66iyar katifar da abbanta yake kai Wanda har gwara tabarma da ita sbd dadewarta dakuma dadewar da abban yayi kwance akanta.

Ginin gidan nasu da 'dakunan gidan gabaki daya sun farfashe alamun ko wane lokaci zasu iya ruguzowa.

Share hawayenta tayi da yagaggiyar atampar jikinta ta miqe zata fita ahankali abbanta yayi magana bataji mai yaceba saita dawo ta zauna tareda kara kunnanta kusa dan taji maiyake fada.

JIDDAH kici gaba dayimin addua Allah ya bayyanamin 'dan uwana kafin nabar duniya.

Sabbin hawaye suka zubo mata tace,
   Abbah dan Allah kadaina maganar daddyn lokoja tunda baidawoba kuma kai ba lafiyane dakaiba.
       Hawaye yafara yana fadin,
   Jiddah inason damqaki a hannun amanane kafin nabar duniya,
Nasani bakida kowa saini,kuma yanda muke dinnan idan na tafi nasan kyararki za'a dinka sbd bakida kowa kuma anai mana kallon almajirai.

Kuka tasaki mai cin rai tana fadin,
Abbah dan Allah kadaka barni tunda Kasan halinda zan shiga idan katafi,
Tun yanxu ana qyamata ana hantarata duk inda naje
Idan katafi bansan yazanyi ba.

Tsit 'dakin yayi sai sheshekar kukanta dake tashi, shima abban nata hawaye yakeyi.

Sundau awa 'daya ahakan kafin ta miqe ta fito tsakar gidansu ta fada 'dakin innarta ta dauko sauran kokon goman data siyowa abban takawo masa ya kurba kadan yace tilas ita ta kurba ko yayane sbd yasan batashaba dan wani lokacin takan kwana biyu ta yini batasha ko taci wani Abu ba sbd basudashi kuma basuda mai basu.
Kofin ta wanke ta jawo kujera ta zauna bakin qofar 'dakin tareda rafka tagumi.



***************

ASALIN LABARI
Ibrahim buba shine cikakken sunan mahaifinta.

Ibrahim marayane datun yana yaro mahaifinsa ya raso sai ya taso dagashi sai mahaifiyarsa inna mero.

Ibrahim yataso cikin gata da kulawa sbd inna mero tana sana'arta ta cikin gida dan haka ta maida duk wani samunta gurin kula da 'danta Ibrahim sbd shikadai gareta har mijinta yarasu.

A makaranta Ibrahim ya hadu da Abdulhameed 'dan dagacin qauyensu.

Sannu ahankali abotarsu tayi nisa sbd halinsu dayazo daya na Neman magana da rashin ji amakaranta.
Abdlhamid shima shi kadai mahaifansa suka haifa,
Mahaifiyarsa ta jima da rasuwa mahaifinsa kawai yarage masa shima babansa yadauki son duniya ya dora masa.

Tsananin son da iyayensu ke nuna musu shiya bada gudunmawa gurin sangarcewa da fara lalacewarsu a qauyen dan tuni suka fara iya tadi da 'yanmata.

Suna ss 2 a secondary Allah ya karbi ran baban Abdulhameed sakamakon guba da  aka sanya masa a abinci sbd son kar6e kujerarsa ta mulkin dagacin gari.

Bayan kwana biyu da rasuwarsa aka kuma shirya yanda za'a kashe Abdulhameed Allah yasa yaji cikin dare ya tattara iya dukiyar babansa daya gani ya gudu.

Bugun gida sukaji tsakar dare dama basuyi barciba sbd Abdul yafada musu komai kuma suma kayansu a shirya suke cikin daren suka tattara sukabar garin.


A wani sabon qauye suka yada zango kuma cikin ikon Allah suka samu karbuwa ba 6ata lokaci suka sayi dan gidansu na ginin qasa mai dauke da daki biyu suka tare.

Inna mero ta hadasu ta riqe bazaka taba sanin ba ita ta haifi Abdul ba dan wani lokacinma tafi nuna sonsa akan Ibrahim.

Su kuwa tuni suka qara sangarcewa sbd hatta kayansu innarsu ke wanke musu duk da sun girma.

Ahankali Rayuwa ta canza musu,rashi ya kunno musu kai dan hatta abinci Neman gagararsu yakeyi ga kuma karatunsu yana neman lalacewa.






Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫
[19:16, 1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱 *_ZUCIYARMU 'DAYA_ .*

漏Mamuh geee

For you my *xinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem_ .

3-4

Fadi tashi inna mero tafara dan batason karatunsu ya lalace bare taga sunason karatun sosai.

Sanar qosai tafara amma Sam 'dan cinikin bazai yi lalurar makarantarsuba.
Canza Sana'a tayi zuwa ta waina nanma babu wani abin kirki,
Qarshe dai aikin sharar makarantar secondary din dake qauyen tasamu inda duk wata ake bata dubu hudu,
Zuwa tayi ta roqi principal akan ahada kudin aikinta na wata uku riqe abari 'yayanta suyi jarabawa.

Haka kuwa akayi harsuka rubuta jarabawar gama secondary suka dasa wani zaman banxar agida sbd babu abin cigaba da karatun nasu.

Shiryawa inna tayi taje qauyensu dasuka baro ta siyar da 'dan akurkin gidanta tadawo tabawa maqwabcinsu dake aikin photocopy a jami'ar birni yasiyo musu jamb form yacika musu.
Da lokacin jarabawar jamb yayi yatafi dasu birni sukayo suka dawo.

Tunda suka dawo suke shirya yanda zasuyi idan suka fasa birni suka hadu da wayayyun yan mata.

Alhmdullillah sunci jarabawa kuma sun samu admission inda suke karantar law dukkansu.

Sauran kudin gidan sune dama inna ta aje dasu sukayi registration da komai dasuke buqata.


Karatu yayi nisa dan tuni 'yayan inna suka waye suka zama cikakkun gayu sbd sun hadu da abokanai 'yayan masu kudi ga yan mata wayayyu sun samu sbd dama dukkaninsu babu baya agurin kyau irin na asalin Fulani.


Inna tsufa yakawo kai yau ciwo gobe lapia amma Sam batayi qasa a gwiwa gurin 'yan sana'oin dazata tallafawa 'yayanta duk da basuda wata Matsala a makarantar sbd abokanansu dan tuni suka daina zama hostel suna gidan wani Senate dasuke karatu da dansa abokinsu kabeer.



****************

Sun kammala degree dinsu sunyi service kuma cikin ikon Allah baban abokinsu kabeer ya samar musu aiki a cikin garin yola.

Dukkaninsu a kotu suke aiki amma kotu daban daban.

Cikin qanqanin lokaci suka rushe gidansu suka maidashi ginin bulo tareda fidda sashe uku kowannensu daya sbd inna ta matsa akan suyi aure.

Yau juma'a dan haka suna qauyen sunzo sbd dama duk weekend acan suke yinsa tareda innarsu.

Kallonsu innar tayi cikin tsananin kauna da kulawa tace,
      Tunda dai nayita cewa ku fidda mata kuyi aure kunqi to nasamo muku matan da kaina.

Ibraheem yayi saurin kallonta zaiyi magana Abdul yarigasa da cewa,
     Inna nifa harna samu mata acan kuma ta yarda zatazo ta zauna anan qauye.

Kallon ibraheem tayi tace,
     Kaifa nima inna nasamu amma marainiyace batada kowa sai kakarta.

To alhmdllh aiba matsala zanyiwa malam shehu magana saisuje suyo komai.


Wata uku tsakani aka sha biki matansu suka tare qauye gidan innarsu.

Matar Abdul 'yar asalin Sudan ce mamarta ta rasu shine tazo Nigeria gurin babanta arashin sa'arta watanta biyu da zuwa ya rasu gurin kammala takardun gadon babanta anan ta hadu da Abdul harsuka fara soyayya batareda tayi la'akari data fisa dukiya nesa ba kusa ba.


Bayan aurensu kowannensu yasamu cigaba sosai domin kuwa dukiya ta fara zauna musu,
Su inna anje makka  ansauke farali.

Fatima matar Abdul ita tafara haihuwa tasamu namiji ibraheem ya nada masa suna TAHEER.

Taheer Nada shekara bakwai Fatima tasake haihu namiji takuma samu wannan karonma ibraheem yayi masa suna ZAID.

har alokacin binta matar ibraheem batada ciki kuma basu daga hankalinsuba sbd ga 'yayanan suna samu daga matar Abdul.

ZAID Nada shekara takwas binta ta haihu ta haifi 'ya mace kyakkyawa.

Sbd murnar haihuwarta harda makka Abdul yaringa biyawa mutane dan ko ibraheem baiyi murnar haihuwar kamar Abdul ba sbd tsananin kaunar dasukewa junansu.
Matayensu har lokacin basusan ba innace uwar Abdul ba.
Sunan inna Abdul yasawa jaririya amma ina tace Sam amaidasa sunan mahaifiyar Abdul data rasu wato MAIJIDDAH.





Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫
[19:18, 1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱 *_ZUCIYARMU 'DAYA._*

漏Mamuh geee

For you my *zinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem_

5-6


Tsakanin Jidda da taheer qauna ce sosai dan yana tsananin ji da ita fiyeda komai abinda kawai ke rabasa da ita shine idan zasu makaranta shida ZAID.

Zaid ba ruwansa da Jidda sbd shi haka yataso wani irin miskili dashi ba Jidda kadaiba shi babu ruwansa da kowa kullum yana lafe agurin mamarsa sai kuma inna dan da farko an dauka baida lpia ne saidaga baya aka gano lpiyarsa klau tsabar miskilancine ke cinsa.

Kyawu kuwa tsakanin Jidda,taheer da zaid baka iya tantance wayafi sbd dukkaninsu farare ne hardai zaid daya 'debo fuskar mamarsa Zak shiyasa ma wani zubin ana cewa yafisu kyau.


Taheer ya gama primary zai shiga secondary kenan akayiwa babansu Abdul transfer zuwa lokoja.
Sosai suka shiga damuwar haka saida inna ta basu qwarin gwiwa sosai tukuna suka iya rabuwa Abdul ya kwashi su taheer suka koma lokoja.


Shekara daya a lokoja arzikin Abdul yayi qololuwar buqasa  dan tuni yatura taheer da zaid new York gurin karatu tun daga kan secondary.

Ibraheem ma arziki yayi gaba dan tuni ya canza musu ginin gidansu zuwa wani irin mansion dan kowa yanxu 6angarensa sama da qasane.

Da sallah dasu dadyn lokoja yazo (a yadda Jidda ke kiransa)dayazo yaga yanda ibraheem ya gyara musu gida saiyace toshi kuma yadau nauyin zuba komai sabo a gidan.

Qauyensu yayi rai dan kuwa tuni ibraheem da Abdul suka zuba musu titina da futilun sola a ko ina.


Dadyn lokoja yayi komai nashirin tafiyar Jidda new York gurin karatu tareda yayunta inna ta hana tace ita mace ce baxa akaitaba.


Sannu ahankali tun Jidda na tunasu taheer harta manta dasu sbd shekaru dasukaja.

**************

 *WATA SABUWA,*

Abdul yakai matakin da aikinsa ya mayardashi qasar Germany.

Yana cikin shirye shiryen tafiya Allah ya karbi ran inna.
Tashin hankalinsu fadarsa zaiyi wuya amma sun shiga matsanancin hali sosai amma ba yanda suka iya sai hakuri.

Rasuwarta da wata 'daya ya wuce Germany cikin alhinin rabuwa da 'dan uwansa, amininsa abokin rayuwarsa.
Hakama su Fatima sunyi alhinin rabuwa da junansu hardai Jidda da Fatima ke masifar sonta.


Isarsu Germany kenan andaukosu daga airport ahanyarsu ta isa gidansu suka samu mummunan hadarin dayayi sanadin ran Fatima nan take shikuma yasamu miyagun raunika da kaririyewa tareda shefewar qwaqwalwa.
Ma'aikatarsu tanan Germany ita tadau nauyin komai nasa bayan sun sanar da 'yayansa dake new york.




Wata 'daya biyu babu waya daga alh Abdul,
Hankalin Ibrahim yayi masifar tashi ga wani tashin hankalin dayake ciki na aikinsa daya rasa saboda mahassada dasuka sakasa gaba.

Kudinsa na banki sunyi qasa sosai gashi babu inna babu abdul.

Lokaci yaja sosai talauci kuwa yayi masa wani irin daurin goro dan takai komai nasa yasaida babu abinda yarage nasa sai gidan dasuke ciki.

Jidda ta zama yanmata tana karatu a makarantar gwamnatin cikin qauyen nasu duk da sai innarta tayi alalan saidawa ake samu aci dakuma kudin lalurar bokonta.

Tanada shekara sha shida ta kammala secondary dinta Wanda tasan babu 'dori daganan sbd babu datayi musu kanta.

Tsanani damuwar rashin sanin inda dan uwansa yake hadi da talauci sun taru sun sakar masa ciwo
Abu kamar wasa saiga ciwo sosai Danko tashi baya iya yi.


A Daren wata talata suna barci tsakar dare gobara takama gidansu sosai

Jama'a sun kawo 'dauki sun fito dasu saidai ana fito dasu Allah yadau ran innarta.



Sun shiga tsananin Rayuwa itada abbanta da tuni ciwo ya qarasa samun guri ajikinsa Danko maganarsa yanxu bata fita said a qyar.

A cikin qonannan gidansu suke rayuwarsu itada abbanta sbd basuda gurin zuwa basuda mai taimaka musu duk da taimakon dasuka ringa yiwa jamaa dasunadashi.






Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫
[21:20, 1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱 *_ZUCIYARMU 'DAYA._*

漏Mamuh geee

For you my *xinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem_

7-8

Rayuwa tayi musu tsanani sbd rashin abinci dakuma ciwon abbanta,ita sutura basama maganarta dan bata ita sukeba.

Aikin wankau tafara yiwa yan qauyen ana biyanta naira biyar a duk kala 'daya.
Da haka take samo musu koko kullum suna sha idankuma tasamu wankin da yawa har da 'dan qosai ko waina take hadowa abbanta dashi, idan kuma batasamu da yawa saidai tabarwa abbanta yasha.

Abbanta bayada zance kullum sai adduar Allah yakawo masa dan uwansa idan har yana Raye.

Takanyi qoqari ta lallashesa idan yafara kukan rashin 'dan uwansa.
Duk lokacin dayayi wannan kukan takanji haushin da tsanar dadyn lokoja da iyalansa naqin waiwayarsu duk da ita bazata iya tuno fuskokinsu ba bare sunayen 'yayansa sbd tun tana yarinya suka rabu.

Shekararsu biyu kenan basuda wata madafa dan tuni tsufa yayiwa abbanta raga raga daga kwancen dan yanxu takai ko tashi baya iyayi yafi shekara akwance.

Jidda farace sosai ada amma wahala,yunwa tareda yunwa sun dafar da ita ta qanjame banda qashi da manyan idanu babu abinda yayi saura a fuskanta.


****************

Sauke taguminta tayi tareda share hawayenta sbd sallamar da akayi.

Wankine aka kawo mata mai uban yawa ta karba babu 6ata lokaci tafara sbd takai abata kudin takarbowa Abba maganin gargajiya gurin mal dauda.

Yini tayi darzar wanki amma bata gamaba sai gab da magariba.
Alwala tayi tayi sallah,duk jikinta ciwo yake sbd wankin harda zannuwan gado.

Ataqaice dai da yunwa suka kwana sbd ba'a bata kudinba sai da safe idan kayan sun bushe takai.

Da daddare ciwon abbanta ya qara tsanani tashi zaune tayi tareda 'Dora kanta kan shimfidarsa ta dingi rusa kuka mai ban tausayi.

Duk duniya babu abinda yakeso sama da 'yarsa tun lokacin data fado duniya,
Dama yana dannewane sbd tsananin son da Abdul yake mata.
Yanaso yarsa tasamu madafa,
Gata mace kuma yarinya dan yanxu shekarunta goma sha takwas.
Ako yaushe hakan kesasa kuka  sosai.

Daqyar sukaga safiya tayi
Sallah kawai tayi ta kwashi kayan takai aka bata naira dari.

Gurin mai magani taje daqyar yabata na sittin taje tasiyo kokon ashirin ta rage sauran ashirin dan siyan kokon gobe.

'Daga kansa tayi ta fara basa kokon ahankali amma saitaga kamar baya shiga.
Yawu ta hade dakyar ta kuma basa kunun taga yadawo.

Batasan sanda tayi wurgi da robar kokonba ta girgizasa da qarfi tana kiran sunansa da mugun qarfi.

Abba,abbana, abbana ka bude ido kaji,
Abbana idan kanasona ka bude ido,
Abba nidai kabude ido inason ganinka ahaka.
Abba dan Allah ka tashi.

Idanuwanta sun bushe tsaf ba hawaye sai jajir da idanun sukayi tsabar tashin hankali.

Zabura tayi da qarfi tayi hanyar waje da gudu ko gani batayi.

Karo tayi da mutum a tsakar gidan nasu tayi saurin ja da baya cikin tsoro tareda qurawa fuskarsa ido.

Dattijone fari tas da Hutu ya ratsa fatarsa duk da tsufansa.,
Kamanninsa suka shiga dawo mata tun lokacin tana yarinya.,

Saurin ja da baya tayi tana masa kallon tsana.

Hawayene kwance a fuskarsa suna kwarara shima kallonta yake cikin jin haushin kansa da baqin ciki murya na rawa ya nunata yace,
        Wannan ce jiddana?
Jiddata uwata,
Ina Raye jiddana takoma haka.

Wanda yakawosu har cikin gidan yace,
 Kwarai kuwa alh wannan Jidda ce.

Share hawayenta tayi cikin dakewar zuciya tace,
         Ku su wayene?
Me kuke nema anan?

Kyakkyawan balaraben saurayin dake tsaye tun shigowarsu yana 6ata fuska yace,
         Dad inaga fa ba nan bane mutafi tun wata cutar bata kuma kamaka ba acikin wannan gidan.

     Ko kallonsa batayiba shi da yayi maganar takalli idris 'dan maqwaftansu daya kawo baqin gidan tace,
      Idris ka kaisu gidan dasuke nema dan nan gidan mu bamada kowa aduniya daxai ziyarcemu.

Jiddah kunada kowa,
Kunada gata,
Ni nan nine kowanku kune kowana,
Jiddana nine dadynki, DADYN LOKOJA.

Rintse idanu tayi hawaye suka gangaro mata sbd jin ciwon zancensa.

Tarin abbanta suka jiyo da qarfi.
Juyawa tayi da gudu tayi dakin cikin farin ciki.
Kansa tayi tana fadin,
    Abbana bakabarni ba.
Abbana kada ka barni dan Allah.

Ahankali ya bude idanunsa basu sauka ko inaba sai akan dan uwansa abdulhameed.






Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫
[21:21, 1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱 *_ZUCIYARMU 'DAYA._*

漏 *Mamuh geee*

For you my *zinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem_

9-10

Rungumosa dadyn lokoja yayi yaba sakin kuka duk da manyancinsa yana cewa,
      Kaicona ni abdulhameed Dana kasa dawowa ga dan uwana harya shiga wannan matsanancin halin,
Arzikina bayada amfani sbd dan uwana jinina da 'yata suna kwana cikin ciwo da yunwa yatashi cikinsu.

Shima abbanta kuka yakeyi yana cewa Allah nagode maka daka cika burina 'daya,
Dayan kuwa koban gani ba nasan dan uwana zai cikashi.

Share masa hawaye yayi yace,
        Ibraheem kuka yaqare mana insha Allah tunda muna tareda juna domin na tabbatarda rabuwarmu ba alkhairine agaremuba sbd munga ishara.
Allah kesonmu atare shiya tsaga jininmu da zuciyoyinmu yasaka mana qaunar juna tun muna yara dan haka bazan qara rabuwa dakaiba dan uwana.
Kobayan ranmu nasan zuriar my zasu dorar da wannan qaunar da amincinmu.


Da kansa yasa yasaka 'dan sauran qarfinsa ya dauki 'dan uwansa yayi mota dashi.

Wata babbar private asibiti suka kaisa kai tatsaye aka karbesa tareda basa kyakkawar kulawa.
Babu Wanda yabar qofar dakin acikinsu  su uku din,
    DADYN LOKOJA, TAHEER DA JIDDAH .

Qarfe uku akace su shiga ya farfado.

Kallon dadyn lokoja yayi tareda kallon Jidda dake raku6e tana kuka yace,
         'Dan uwana tunda kabarni banida buri na biyu ne,
Na farko ganinka, na biyu ganin na aurar da Jidda sbd tasamu madafa dakuma gobenta idan babu ni.

Buri daya yacika dan haka koban ga cikar na biyunba nasan kai uba nagari ne ga jiddana.
Nagode sosai dan uwana amma kasani inaji lokacina yayi dazan barka.

Ibraheem bazaka barni sbd banida kowa bayankai,
Inna ta barmu,Fatima ta barmu,binta ma tabarmu Yaya kake tunanin zan rayu idan kaima ka barni.
Kafada min burinka,daya ya cika yanxu insha Allah zancika ma dayan dan yanxu a masallacin asibitin nan zan daur auren taheer da Jidda.
Burina nima danake roqon Allah yacikamin shine Allah ya barmin kai idan kuwa lokacin tafiyar takane yazo ina roqon Allah yadau ranmu atare.


Fita yayi tareda daga wayarsa yakira lauyansa basheer,
Cikin minti biyar sai gashi
Kallonsa yayi yace,
      Barr bashir na mallakawa 'yata Jidda Rabin dukiyata.
To kawai Barr yace tareda miqa masa takardu yasaka hannu suka dunguma masallacin asibitin dan daura auren Jidda da taheer.


Cikin rashin fahimta taheer yace,
   Dady nifa bangane mai kake nufiba,
Abune mai sauki taheer domin kuwa auranka da Jidda zan daura ayanzun nan kuma idan har nina haifeka kazakace qalaba.

Wani irin mummunan zufane ya tsinke masa sbd masifar datake shirin afka masa gashi dady ya rufe bakinsa.

Abbanta na kwance adakinsa yanaji ta loudspeaker har aka gama daura auren.

Hawayen dadine suka gangaro masa ya kalli Jidda dake raku6e ianuwanta sunyi jajir sbd ita yanxu ko hawayen babu sun Riga sun qafe mata.

Murya asarqe yace,
Jiddana zo kusada abbanki.
A nutse ta matsa ta zauna bakin gadon.
Hannunta ya riqo yace,
 Jidda Allah yayi miki albarka keda zuriar dazaki Tara gaba,
Jiddana Allah yabaki hakuri da juriya,
Allah ya hadaki da alkhairai arayuwarki.,
Jiddana kizamo mai juriya da biyayya sbd Rayuwa akwai qalubale atattare da ita.,
Jidda kiyimin alqawarin yin biyayya da jajircewa ki zama 'ya da mata tagari.
Jiddana Allah yazama gatanki ya tsareminke daga mummunar kaddara.

Dago jajayen idanunta tayi takallesa dakyau kafin ta daga kai tace,
 Abbana zanyi duk abinda kace har qarshen rayuwata koda kuwa naman jikina za'a riqa diba.

Jiddana....kasa magana yayi sbd kukan tausayin 'yarsa wadda tun yanxu ya hango bushewar zuciya atattare da ita sbd yasan taga Rayuwa amma yasan qalubale na gaba idan ta rasashi.
Allah yabaki ikon jurewa jiddana.

 Ameen tace ahankali.

Dadyn lokoja ne yashigo dakin yakalli 'dan uwansa saiyaga yana murmushi.
Matsawa yayi kusa dashi zaiyi magana abban yarigasa da cewa,
        Nagode 'dan uwana.

Daga fadar haka kuwa sai Kalmar shahada.


**************

Bugawar zuciyane Yakama dadyn nan take ya zube kan 'dan uwansa yana kiran sunansa kafin shima ya fice hayyacinsa akayi emergency dashi.

Kallon gawar abbanta tayi tareda tofa masa addua batareda tayi kuka ba saidai wani mugun nauyi da zuciyarta tayi mata dan daza'a bude zuciyarta lokacin to dutsi za'aga takoma.

Awa biyu dadyn ya farfado ya buqaci ganin Jidda da Barr bashir.
Cire oxygen din da aka samasa yayi murya na rawa yace,
    Bashir ga amanar 'yata,
Kasata makaranta tayi karatu cikin dukiyarta dana bata,.
   
    Jiddana ga bashir nan ki riqesa duk matsakarki ki Sanar masa.

Kallon dadyn tayi cikin tausayin shima rasashi zatayi kenan.

Taheer ya kalla yace,
    Taheer ka riqe Jidda tamkar zaid,
       Banyafe ku yakice Jidda daga cikinkuba kaida zaid.
      Ka lura da zaid da jiddata.
Ka........ Sarqewa muryarsa tayi kafin shahada ta fito daqyar shima yace ga garinku nan.


Sulalewa Jidda tayi qasa a some yayinda Barr yayi kanta da sauri shikuwa taheer kan dadynsa yayi.

 *BADA QALA KENAN...*



Mamuh geee馃寱馃寫馃寱馃寫
[21:25, 1/1/2018] 鈥�+234 813 039 8818鈥�: 馃寫馃寱 *_ZUCIYARMU 'DAYA._*

漏Mamuh geee

For you my *zinnie*

 _Bismillahir-rahamanir raheem_