Showing posts with label Nasiha. Show all posts
Showing posts with label Nasiha. Show all posts

Saturday 3 November 2018

Ko Ka San Yadda Za Ka Ci Ribar Zama Da Mace?

November 03, 2018 0


Hakika ba za ka taba samun jin dadin zamantakewar aure a cikin gidanka ba har sai ka kiyaye wadansu dabi’u da za ka mu’amalanci matarka da su, don haka sai mu kiyaye su. Hakika su mata suna son lallashi da ja a jiki, kuma suna son a dinga cewa ana sonsu ana kaunarsu. Don haka kada ka dinga yi musu rowar fadar haka, idan kuwa ka yi rowar to ka sanya hijabi tsakanin ka da ita na samun karancin soyayya da kauna.

Ka sani cewa su mata ba sa son mutum mai tsananin takurawa, idan ka fahimce su, suna yi wa mutum rarrauna hidima. Don haka kowacce sifa ka a jiye ta a gurin da ta dace domin hakan shi zai fi jawo kauna da nutsuwa a tsakaninku. Hakika su ma mata suna son irin abin da namiji yake so daga gurin mace, kamar daddadan kanshi, magana mai dadi, kyakkyawar shiga, tashin kanshi da dai sauransu.

To don haka ka sifantu da dukkan wadannan halaye a dukkan yana yinka. Ka sani cewa gida wata masarauta ce ta mace wadda take jin cikyakkyen iko a cikin ta kuma take jin cewa ita ce shugaba a cikinsa. To ina jan kunnenka duk wani majidanci da kada ka kuskura ka rusa wannan masarauta, kana mai nuna mata cewa ita ba kowa bace ko kuma gidanka ne sai yadda ka so sai abin da ka so, idan ka yi haka to ka tumbuketa daga kan sarautarta, kuma mai mulki bashi da wani abokin gaba a duniya fiye da wanda ya sauke shi daga kan mulkinsa.


Dukkan mace tana son ta yi wa mijinta hidima amma kuma ba ta son ta rabu da ‘yan’uwanta, to kada ka yi kokarin raba ta da danginta, ta hanyar ba ta zabin ko kai ko danginta, domin idan ta zabe ka a kan danginta to babu shakka za ka dawwama cikin bakin ciki da bacin rai da za ka dinga samu daga gare su. Hakika ita mace an halicce ta ne daga kashin hakarkarin namiji karkatacce, wannan kuma ba aibu ba ne a gare ta, shi ne ma kuma sirrin kyawunta da kuma jan hankalin da take yi wa maza, don haka kada ka hayayyako mata a lokacin da ta yi wani kuskure kana kokarin gyara ta da karfin tsiya sai ka karyata, karya ta kuwa shi ne sakinta.

To kada kuma ka kyale ta ta yi abin da ta ga dama ko kuma ta ci gaba da yin kuskuren da sunan a karkace take, domin sai ta bijire maka daga karshe ta ki yi maka biyayya, kai dai ka kasance da ita baina-baina. To kuma ka sani cewa su mata sun dabi’antu a kan saba wa miji da kuma yi masa butulci. Idan da za ka kyautatawa mace tsawon shekara ko zamani, sai wata rana ka munana mata, za ta ce me ka taba yi min?.

To kada a wannan hali na ta ya sa ka kyamace ta gaba daya, domin idan ka kyamaci wannan dabi’ar daga gare ta to za ka yarda kuma da wasu halayenta masu kyau. Ita mace ba kamar namiji ba ce, tana rayuwa ne cikin rauni na jiki dana ruhi, saboda haka ne ma Allah ya dauke mata wasu daga cikin farillan da ya wajabta mata a wani lokuta saboda wannan rauni na ta.

Dubi yadda Allah ya dauke mata sallah a yana yi na haila, ya jinkirta mata rama azumi har sai ta gama haila, to ka saukaka mata umarninka da hane- hanenka a wannan yana yi kamar yadda ubangijinta ya saukaka mata farillansa. Ka sani cewa ita mace baiwa ce a hannunka, don haka ka ji kanta ka tausaya mata ka kuma dauke kai dangane da rauninta sai ta zamar maka kyakkyawar abokiyar zama kuma mace ta gari. Allah ya bamu ikon zama da iyalanmu lafiya.

Source@ Arewablog

Wednesday 24 October 2018

Yadda Auren Amarya Ya Kusa Mutuwa Saboda Amfani Da ‘A-Cuci-Maza’

October 24, 2018 0



Akwai wani saurayi  mai suna Faruk (ba sunansa na gaskiya ba) da yake neman wata yarinya da aure mai suna Ramlat (ita ma ba sunanta na gaskiya ba).  Suna gari daya ne amma ba unguwarsu daya ba.

Ramlat ba ta wuce shekara 19 ba, budurwa ce mai takama da ji da kai.  Hasali ma ma yarinya ce da ba kowane namiji take kulawa a rayuwarta ba. Hakan ya sa samari da yawa suke  shakkar yi mata magana ko  hulda da ita.

Duk da Ramlat ta fito ne daga gidan talakawa, amma takan dauki kanta tamkar wadda ta fito daga gidan masu kudi. Dalili shi ne saboda yanayin shigarta da yadda take ji da kanta musamman idan ta shiga cikin jama’a ko tana tafiya a kan hanya. Yadda take tafiyar kasaita d ji-ji-da-kai, na ba mutane mamaki musamman wadanda suka san asalinta.

Sai dai iyayenta mutanen kirki ne, ita ce dai ta mayar da kanta haka. Tamkar karin maganar nan da ke cewa  albasa ba ta yi halin ruwa ba

Ramlat ta samo irin wannan dabi’a ce lokacin da ta yi karatu a wata sakandaren ’yan mata ta kwana, inda ta hadu da wadansu kawaye da suka fito daga gidajen masu kudi.  Irin zaman da Ramlat ta yi da wadancan kawaye ne suka canja mata ra’ayi, inda take ganin ta fi karfin kowa, muddin namiji ba ya da kudi, to ba ta da lokacinsa. Ta dauki girman kai ta dora wa kanta, inda duk saurayin da ta ga ba ya da kasaitacciyar mota, to da wuya ta saurare shi.

Ramlat ta ci gaba da kasancewa a irin wannan hali har  tsawon lokaci. Sai dai abin da ba ta fahimta ba shi ne, ta shafe shekara da shekaru ba ta yi aure ba, inda shekaru suka fara yi mata nisa. Duk kyale-kyalen da take takama da su, sun fara gushewa.


Duk kawayen da take gani ba su kai ta waye ba, kuma ba su dauki rayuwar duniya a bakin komai ba, sun yi aure.  Wadansu ma sun haihu, suna zaune lafiya a gidajen mazansu.  Ita kuwa kullum sai caba kwalliya da kwambo ana ziyartar gidajen kawaye masu hali.

Sannu a hankali kawayen nata da take kai wa ziyara iyayensu suka fita da su kasashen waje don su ci gaba da karatu. Ita kuwa iyayenta talakawa ne, ba su da halin da za ta iya ci gaba da karatu a gida ma balle su tsallaka da ita kasashen ketare.

Ba a dade ba, mahaifin Ramlat ya kwanta rashin lafiya, daga baya ya rasu. Aka bar ta a karkashin kular mahaifiyarta, alhali gidan da suke zaune a ciki ma na haya ne.

An kai lokacin da kyar suke iya biyan kudin haya. An yi sa’a ma mai gidan yana da mutunci, ya fuskanci halin kuncin da suke ciki ne inda hakan ya sa ya daga musu kafa.

Rayuwa ta fara yi mata nisa, har ta doshi shekara 30 ba wani aiki take yi ba, kuma ba ta yi aure ba, sannan mahaifiyarta girma ya fara kamata. Tun bayan rasuwar mahaifinta, mahaifiyarta ta shiga wani hali na gwagwarmayar kula da Ramlat. Hakan ya sa ta yanke shawarar ba za ta sake yin wani aure ba har sai ta aurar da ’yarta Ramlat.

Za mu ci gaba.


Souce@ Arewablog.Com